Wednesday, June 20, 2012

KADUNA BA LAFIYA


HADEJIA A YAU! Rahotanni daga jihar Kaduna ya nuna cewa Har yau rikici bai lafa ba dukda Dokar hana zirga zirga da aka sanya a Jihar. Ko a yammacin yau anji Karar harbe harbe da kone kone a yankin Badarawa,Unguwar yero da kuma wasu sassa a Unguwar Dosa. Wani ma'aikacin Gidan Redio ya ruwaito cewa An harbi wani yaro a Gabansa, Bayan an kaishi asibiti daga bisani ya cika. Allah ya mana maganin wannan masifa! Kwanaki hudu dai kelau ana zaman Dar dar a Jihar Kaduna Rikicinda ya rikide ya zama na kabilanci da Addini.

No comments:

Post a Comment