Tuesday, June 19, 2012


HADEJIA A YAU! An sake sanya dokar awa Ashirin da hudu a Jihar Kaduna Sakamakon Tashin hankalin da ya biyo bayan harin bom din da aka kai a Zariya da kaduna. An samu labarin Jiya da dadare matasa sunyi ta kai farmaki a junansu da niyyar daukan fansa. Haka kuma yau ma fada ya barke a Unguwanni daban daban a kaduna. Dukda dokar hana zirga zirga da Gwamnan jihar ya saka. A Damaturu ma ta jihar Yobe rikicin ya lafa kuma suma ansa dokar Hana zirga zirga. Mutanen garin dai sun bayyana wannan abin a matsayin Gazawar Gwamnatin tarayya na kasa magance matsalar tsaro.

No comments:

Post a Comment