![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEhN08qUXWDXUkrUu3vW7V9lNUMTghDZQbe_grIh_UcCpU-oQrw9Yrct1eOqvOVY0-xF16OIqYbfG9UMS6VX3cgvPaOoyCj6jPFMNCSFGKebMHNGCVoX7e8ybASZY-nGZ9UaOsRoVs1C3LBt/s400/Kabarin+Sambo.jpg)
HADEJIA A YAU! Sarkin Hadejia Sambo shine ya karbo Tutar Musulunci a gun Usman Dan fodiyo! Yayi mulkin Hadejia tun daga 1808 zuwa 1848. Allah ya masa Rasuwa a Mai-Rakumi. Kuma anan kabarinsa yake! A cikin 'ya'yansa akwai wadanda sukayi Sarautar Hadejia a lokacin yana Raye. Kamar Garko Gambo 1845t-1847, Abdulkadir Dan Sambo 1847-1848. Sannan Sambo yaci Gaba da Mulkin Hadejia kuma ya Rasu a wannan shekarar. Sai kuma Dansa Buhari Sai Ahmadu sannan Buhari Sai jikansa Umaru Dan Buhari. Sai kuma Dansa Haru Bubba. Allah ya Gafarta musu.
Allah yaji kansu.
ReplyDeleteAllahu Akbar! Sambo sababa Hadejia
ReplyDelete