![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEhN08qUXWDXUkrUu3vW7V9lNUMTghDZQbe_grIh_UcCpU-oQrw9Yrct1eOqvOVY0-xF16OIqYbfG9UMS6VX3cgvPaOoyCj6jPFMNCSFGKebMHNGCVoX7e8ybASZY-nGZ9UaOsRoVs1C3LBt/s400/Kabarin+Sambo.jpg)
HADEJIA A YAU! Sarkin Hadejia Sambo shine ya karbo Tutar Musulunci a gun Usman Dan fodiyo! Yayi mulkin Hadejia tun daga 1808 zuwa 1848. Allah ya masa Rasuwa a Mai-Rakumi. Kuma anan kabarinsa yake! A cikin 'ya'yansa akwai wadanda sukayi Sarautar Hadejia a lokacin yana Raye. Kamar Garko Gambo 1845t-1847, Abdulkadir Dan Sambo 1847-1848. Sannan Sambo yaci Gaba da Mulkin Hadejia kuma ya Rasu a wannan shekarar. Sai kuma Dansa Buhari Sai Ahmadu sannan Buhari Sai jikansa Umaru Dan Buhari. Sai kuma Dansa Haru Bubba. Allah ya Gafarta musu.
No comments:
Post a Comment