Showing posts with label Full. Show all posts
Showing posts with label Full. Show all posts

Wednesday, February 5, 2014

EMIRE OF HADEJIA ALH.HARUNA ABDULKADIR.

Emir of HADEJIA Alh. Haruna Abdulkadir ruled from 1950, before he was appointed as Chiroma as Distric head of Guri at the age of 12 in 1921, he experienced a poor health for some years, during which the emirate council ischaired by successive Galadimas, the decendent of Jaji on his behalf who takes charge on the administration of HADEJIA town, just like Sarkin Arewa is district head of Birniwa and Sarkin Dawaki administers kirikasamma district.

But while previously, during colonial period, the Tafida administered Kafin Hausa as district head, until more recently when it was given to Chiroma, a son to the Emir. Fallowing Chiroma’s appointment as a chairman of the Kano state local government service commission he was unfortunately obliged to reside at Kano city, leaving Kafin Hausa to be administered by his deputy while he retain the title.

The old emirate council from 1971 – 1975meet more frequently under the chairmanship of the Galadima Yusuf and Adamu, the major responsibilities of that administration rested firmly with Dan’iya,M. abdulkadir Maidugu, himself a grandson a grand of the Emir Abdulkadir and formally Sarkin Auyo and district head of Auyo, he represented HADEJIA inthe Federal House of Assembly. In his return after the abolition of a civilian rule, he was appointed Senior Executive Councillor of the Emirate council in charge of finance, the native administration,works, rural water supplyand community development.

TheTafida alh. Abdulkadir Maigari, another grandson of the emir Abdulkadir was appointed a councillor in charge of Agric and Natural resourses.The Danburan muhammadu Hurdi……………….

.(Culled from “Local Government at Hadejiia 1977” By M. G. Smith)
By Ma'aji I Abubakar.

Thursday, November 21, 2013

TARIHIN HARUNA UJI. DA WAKOKINSA. KASHI NA DAYA (1).

Alh. Haruna Uji Hadejia.

Hadejia A yau! An haifi Alh. Haruna Uji A Unguwar Gandun sarki dake cikin garin Hadejia, a shekarar (1946). Sunan Mahaifinsa Mallam Ibrahim, Malami ne kuma shine Limamin Gandun sarki. Sunan Mahaifiyarsa Zainabu itama mutumiyar Unguwar ce. Anan ya tashi yayi wayo. Yana kimanin shekara shida mahaifinsa ya sakashi a makarantar Allo dake kofar gidansu, a gun wani Malami da ake kira Mallam Alhaji.

Haruna Uji ya shafe wajen shekaru uku yana wannan Makaranta a Gandun sarki, daga nan suka tashi da malaminsa zuwa garin Birniwa wanda take gabas da Hadejia, mai nisan kilo mita 45. Sun kwashe shekaru kamar biyu suna karatu da sauran Almajirai, anan Uji ya samu karatu mai dama.

Bayan nan suka bar Birniwa suka dawo Hadejia suka ci gaba da karatu a Gandun sarki. Wannan yasa ya samu karatu mai dama fiye da sauran yara musamman wadanda suka zauna a gida basu fita wani guri neman Ilmi ba. A wannan lokaci Mallam Alhaji yakan sa Uji ya kula da yara tare da koya musu karatu. Haruna Uji ya bar makarantar Allo yana dan shekara goma sha biyu, bayan ya samu karatu mai dama.
Hadejia A yau!

1.1, ASALIN INKIYAR HARUNA UJI..
Sunansa na yanka Haruna, yaci sunan wan Mahaifinsa, wato Mallam Haruna. Mallam Haruna mai sunan Uji yana da mata mai suna IYA KURA, Lokacin Uji yana karami matan kanin Babansa suna masa wasa suna ce masa Mijin Iya Kura, Mijin Iya Kura' A wannan Lokacin yara kannensa basu da baki, sai suke ce masa, Ujin Iya Kura. Maimakon Mijin Iya Kura. Wannan shine Asalin inda Haruna Uji ya samo Inkiyar Uji. Tun ana danganta sunan da Iya Kura har aka daina ake cewa Uji.

1.11, SIFFAR HARUNA UJI.
Haruna Uji baki ne, mai matsakaicin tsawo, yana da jiki matsakaici, ga farin hakora da bakin gashi, yana yawan barin gashin baki, ga magana (Idanu) haka kuma, ma'abocin barin suma ne, yana da Murya mai zaki da kauri kadan, kuma Gwanin Ado ne, da manyan kaya na sarauta. Kuma yakan saka 'yar shara, musamman lokacin zafi.

Alh. Haruna Uji mutum nd mai fara'a da kyauta, domin abin hannunsa bai rufe masa ido ba. Yana da raha sannan kuma bashi da wata nakasa a fili.

2.0, SANA'OIN HARUNA UJI..

2.1, Farauta da Noma.
Bayan Haruna Uji ya bar makarantar Allo, ya fara zuwa Daji da nufin farauta. Wadda itace sana'arsa ta farko, wanda ya fara, kuma ta sanyashi jarunta inda ya zama bashi da tsoro. Kuma a nan ne ya samu tambaya wato lakani na tsare kai.

Bayan farauta Haruna Uji Manomi ne, ya fara aikin gona ne da taya mahaifinsa, domin neman tabariki, wannan tasa yasan harkar noma wanda har yake noma gonar kansa.

2.2, Sana'ar Tukin Mota (Direba)
Alh. Haruna Uji yayi Sana'ar Tukin mota, wanda ya fara da Yaron mota a gun Mai gidansa wanda ake kira da suna Jibrin Dan Amingo. Jibrin Dan Amingo dan Asalin Danbatta ne ta Jihar Kano. Haruna Uji ya shafe shekaru da dama yana sana'ar yaron mota. Tukin mota ne sana'arsa ta farko da ta fara fitar dashi wani gari da nufin zama. Suna aiki ne tsakanin Kano da Hadejia.

Kuma a wannan lokacin suna zaune ne a garin kano a Tudun wada. Amma duk abinda ya taso a gida dashi akeyi, musamman aikin gona da bukukuwa da sauransu.

2.3, Sana'ar Waka.
Haruna Uji bai gaji waka ba, domin Mahaifinsa Malami ne, kuma ko a wakarsa ta Gurmi ba Haramun ba yana cewa:-
"Ni Haruna dan Mallam nake, Waka ta ba ta gado bace"

Saboda haka tun farko Haruna Uji ya riki waka ne a matsayin nishadi, domin ba wanda ya koya masa waka a matsayin Sana'a.

Haruna Uji ya fara ganin Gurmi ne a gun wani ma'aikacin titi wanda sukayi aiki a hanyar Mallam madori zuwa Gumel, wanda ake kira Dan-mato, a gun Dan-mato Uji ya fara ganin Gurmi da kidansa, shi Dan-mato yana kada Gurmi ne a yayinda suka samu hutun aiki. Yana kadawa yana waka, lokacin Uji yana Matashi, duk lokacinda sukaje kallon aiki sai su tsaya suna ganin kidan Gurmin Dan-mato, wannan tasa kidan Gurmi ya shiga ran Haruna Uji, idan ya dawo gida sai yakan nemi gwangwani da tsirkiya ya hada Gurmi yana kadawa. Har Dan-mato suka hada aikin hanya bai koyawa Uji Gurmi ba, sai dai Uji yana zuwa yana ganin yanda yake kadawa. Wannan tasa Uji ya dinga kwaikoyon Dan-mato tun bai iya ba har ya koya.

Wannan yasa idan yana gurmi yara sukan tsaya suna ji da kallonsa, Wannan shine Asalin koyon Gurmin Haruna Uji. Daga nan sai ya fara tunanin ya samu sanda, da lilo da butar Duma da fatar Damo da Zobe domin ya hada bubban Gurmi.

Farkon lokacinda ya fara Gurmi idan an bashi abu baya karba, don yanayi ne saboda Nishadi. Kuma sau da yawa idan ya fito hira ko ana wani biki na samari da 'yan mata, yakan kada Gurminsa yana waka, samari da 'yan mata suna kallo.

A wancan lokacin yana Gurmi yana aikin Mota, wannan yasa ya fara Gurmi a garuruwa daban daban na Arewacin Nigeria.

Daga nan Uji ya bar tukin mota ya koma kidan Gurmi Kuma ya nemi mataimaka don sunayi su biyu.

Karashe a kashi na 2.
Littafin Muhd. Aji Hadejia

Wednesday, September 18, 2013

CIWON KODA A KASAR HADEJIA! DAGA PHARM. HASHIM UBALE YUSUF.

Hadejia A yau! Daga pharmacy Hashim Ubale Yusufu


Bismillahir Rahmanir Rahim. Assalamu Alaikum.

CIWON KODA A KASAR HADEJIA: A bisa kididdiga, kimanin mutane miliyan talatin (30million) ne ke dauke da cutar Koda a tarayyar Nigeria. (National Association of Nephrology). Yawancin wadannan mutane na mutuwa kuwa katsam daga cutukan da suka shafi makwarar jini da zuciya, wanda ke da danganta da ciwon kodar. Wannan ya nuna cewa kimanin mutane ashirin bisa dari (20%) na ‘yan Nigeria na fama da wannan ciwo, wanda ana ganin alama daga yawan karuwar masu neman tace jini (dialysis). A wasu asibitocin zaka iske kimanin mutane 200 zuwa 300 ke zuwa neman tace jininsu a rana.



Cututtuka da dama na iya jawo ciwon Koda. Manyan dalilan dake hassada wannan ciwo anan karkarar sun hada da ciwo tsutsa (infections), kishirwa da kuma shaye shayen magunguna kai tsaye, Hawan Jini, shan taba da makamantansu.
Ita koda tana taimakawa jikine wajen tace dattin da kan taru a jikin mutum, sannan kuma tana taimakawa wajen tsotse ruwa, da sukari da sauran sinadaran gina jiki dake yawo a jini domin kar su bi fitsari su fice. Kenan zamu iya gani cewa idan har Koda bazata iya yin wannan tatar ba, to kuwa akwai matsala. Babban abun dazai faru kuwa shine, dattin na iya tare kofofin da jini da fitsari zasu bi, daga nan sai a fara kumbura, da kuma samun zazzafan ciwo na fitar hankali a hanyar da fitsari yake bi.




Sau tari zaka tarar mutane na aikin dake sa su zubad da gumi mai yawa, amma babu ruwa a kusa dasu. A kauyuka da rugage, zaka samu rijiyoyi sun kafe, ko kuma zasu sha ruwa gurbatacce, saboda ba inda zasu samu ruwan mai kyau su sha. Wannan bala’i ne.
Sannan kuma, yanzu wani abu wanda yake kamar gasa shine shaye shayen magunguna babu dalili ko kuma babu neman shawarar masana.




Wannan ka iyasa shan gurbatattun magunguna ko na jabu wadanda zasu iya cutar da ita kodar ta daina aiki. Haka kuma shaye shayen maganin gargajiya na daya daga cikin abubuwan da ke jawon wannan ciwo.
Akwai gazawar kayan aiki a asibitocinmu na tace jini da musayar koda, wanda hakan na jawo matsalar kai marasa lafiyar kasashen waje don warkarwa. A inda kuwa babu halin haka, sai addua kenan.

Sunday, April 21, 2013

TARIHIN SARKIN HADEJIA UMARU DAN BUHARI DA ZUWAN SARKIN DAMAGARAM HADEJIA..

Image Hosted by ImageTitan.comHADEJIA A YAU!



SARKIN HADEJIA UMARU: A SHEKARAR 1863 allah ya yiwa Sarkin Hadejia Buhari rasuwa a Yakinsu da sukayi da Gogaram (bade). Ko da aka dawo Hadejia aka binne shi sai Manyan fadawan Hadejia wadanda akwai Amana tsakaninsu dashi Buhari. Kamar SARKIN AREWA TATA GANA DA SARKIN YAKI JAJI suka jajirce Sai an Nada UMARU DAN BUHARI SARKIN HADEJIA. kuma hakan Akayi!


SARKIN HADEJIA UMARU NA BIYU an nadashi yana da shekara Goma sha Takwas (18). Kuma manyan fadawan Mahaifinsa sune suke gudanar da Sarautar tunda shi yaro ne. Kuma a zamaninsa Sarkin Damagaram Tanimu ya kawo yaki Hadejia. Kuma yayi sansani a Arewa da Hadejia daga nan har Jigawar Kasim mutanensa ne. saida yayi kwana Arba'in ana yaki amma Hadejiawa basu fasa wasanninsu na dandali ba. Sannan kuma basu fasa duk harkokinsu na kasuwa ba, su kuma mutanen Sarkin Damagaram suna kaiwa farmaki kauyuka suna kwace musu kaya! Sannan sun hana mutanen kauyuka shigowa Hadejia domin saye da sayarwa. A nan kuma sun hana Makiyaya kiwon Dabbobinsu, Sai sarkin Arewa yasa akayi sanarwa a Hadejia cewa: duk mai dabbobi gobe ya sako su za'a kaisu kiwo, kuma hakan sukayi suka saki dabbobinsu Sarkin Arewa da Mutanensa sukaje sukayi kiwon suka dawo. Ta wajen Dan-Rago kusa da Maficin Sarki.

Da Abin ya ishi Mutanen Hadejia sai suka Sanar da Sarkin yakin Hadejia Jaji, sai ya tara Fadawan Hadejia yace Naji ance Sarkin Damagaram yazo, Yau wajen kwana 40, sukace hakane! Sai sarkin Yaki yace so kuke yazo ya koremu daga Garin?

Da safiya tayi sai sarkin yaki Jaji ya hau dokinsa ya dauki Takobinsa ya fita yacewa sarkin Kofa in ya fita ya rufe Kofar Gari, kuma ko an koroshi karya sake ya bude, idan ya bude masa to zai kashe shi. Sarkin yaki Jaji yaje ya fara baza Mayakan sarkin Damagaram yana korasu, saida ya korasu har Rumfar Sarkin Damagaram ya dawo da niyyar Washegari aci gaba da yaki.

Da sarkin Damagaram yaga anyi haka sai ya tara Hakimansa da fadawa yace gobe zamuci Hadejia da yaki. Suka amsa suna Alwashi, bayan an baje sai Chiroman Damagaram ya samu sarki yace masa Shawara nazo in bayar, sarki ya yarda. Chiroma yacewa Sarkin Damagaram duk garin da mukaje musu yaki basu da sukuni saboda suna tsoronmu, Amma yau kwananmu Arba'in (40) Hadejiawa basu fasa duk abinda sukeyi ba! Kuma mun samu Labarin Sarkin Hadejia bai san munzo ba, yacewa sarki Ina ganin ya kamata ko mu shiga mu yakesu ko kuma mu koma Gida!

Wata rana ana yaki Sai aka harbi dokin Sarkin Arewa! Koda ya mutu sai akaje gida aka dauko wani Dokin aka cire kayan wancan Dokin aka sakawa wanda aka kawo. Tata gana ya koma kan doki, kashe gari ana cikin yaki sai Tata gana ya sauko daga Dokinsa yayi alwala ya koma kan Dokin, to ashe Sarkin Damagaram yana kallon su sai yace Lalle Sarkin Hadejia ya Isa ana yaki ka sauko kayi alwala? Jiya ma an kashe masa Doki amma saida akaje aka dauko wani a gari? Sai Zagin Sarkin Damagaram yace ai ba Sarkin Hadejia bane Yaronsa ne! Sai Sarkin Damagaram Tanimu yace to Ina Sarkin Hadejian? Sai zaginsa yace ai ance yana gida tunda aka fara yakin nan bai taba zuwa ba. Sai sarkin Damagarm yace wa fadawansa Gobe zamu bar Hadejia kar mu tsaya ayi ta kashemu. Saboda Sarkin Hadejia ya raina mu kwananmu Arba'in amma bai taba zuwa anyi yaki dashi ba? Wa yasan me zai mana in ya zo? Amma basu san Sarkin Yaro bane. Washe gari suka juya suka koma Damagaram. Kuma lokacinda sukazo Hadejia Da kaka ne! Anyi girbi Manoma basu gama Tare Amfaninsu ba. Shi yasa suka dade a Hadejia saboda akwai abinci da ruwa a kusa dasu.

SARKIN HADEJIA UMARU Mutum ne mai son Nishadi kowane Lokaci yakan fita Bakin kogi ko Gona Domin Debe kewa. Kuma anyi amfani da wannan Damar inda wata rana ya fita sai aka Rufe Masa Kofa. Koda yazo yaga kofa A rufe sai ya juya ya tafi Chamo ya zauna. Aka nada Kanin Mahaifinsa Sarkin Hadejia Wato HARU BUBBA. 1865-1885. Shi kuwa UMARU DAN BUHARI yayi zamansa a Chamo kuma Ya rasu a shekarar 1920. Allah yaji Kansu Ameen.

HADEJIA A YAU.

Monday, July 9, 2012

TARIHIN KAFUWAR HADEJIA KASHI NA (1)


HADEJIA- TARIHIN KAFUWAR Hadejia Ya
farune daga wani maharbi mai suna Hade, a
yawon farauta da yakeyi ne wata rana yana
tafe da karyar sa sai tayi nisan kiwo ko da
tazo sai yaga duk jikinta da ruwa, sai yayi
mamakin hakan har ma sai yabi sawunta.
Koda yaje sai yaga kogi kuma ga tsuntsaye
suna shawagi a gurin. Sai ya yanke
shawarar zama a wannan gurin, kuma
hakan yayi. Anan ya zauna yayi bukkarsa
yake harbe harben Namun daji kuma yayi su
wato kamun kifi. In ya kashe namun daji sai
yaje ya sayar da fatun. Harma ya dauko
Matarsa wato Jia ya dawo da ita wannan
gurin. Kuma mutane sai suke zuwa sayen
fatu da nama a wajensa. Duk wanda yazo
gurin sai yayi sha'awar zama a gun, haka
nan gari ya fara bunkasa wasu maharba,
wasu masinta, wasu kuma mafarauta. Sai
gari ya kafu kowa yazo wucewa sai ya yada
zango a garin. To kasancewar gari sai da
shugabanci ne yasa shi Hade ya zama
shugaban garin, duk wanda zaije sayen fatu
ko nama sai yace na tafi garin Haden jia.
Wato ana masa lakabi da sunan matarsa. To
sakamakon takaita kalma irin ta Bahaushe
sai aka dunkule sunan ake cewa Hadejia.
Kuma bayan zamanin wannan mutumin
Hadejia taci gaba da zama gari kuma tare da
shugabanci wato mulkin Habawa. Kuma a
lokacin akwai kananan Garuruwa masu cin
gashin kansu kamar Rinde, yayari, wunti,
Anku da dai sauransu. Wadanda suma suna
da nasu sarakunan a wannan Lokacin.
Amma yanzu duk unguwanni ne a cikin
garin Hadejia. Kuma Hadejia sunyi
sarakunan Habe guda talatin da biyu(32)
amma sunan mutum uku ake dasu wadanda
sukayi mulki kafin zuwan Fulani. 1, BAUDE 2,
MUSA 3, ABUBAKAR. Kuma a lokacin
Abubakar fulani sukazo kasar Hadejia, kuma
shine ya basu masauki a Hadejia Lokacin
Hadejia tana karkashin Daular Borno, kuma
ya nada Umaru a matsayin Sarkin fulanin
Hadejia. Wato kafin Jihadin Shehu usman
dan fodiyo. Kuma har yanzu fulanin sune
suke sarautar Kasar Hadejia.
A GABA ZAN KAWO MUKU TARIHIN
SARAKUNAN FULANI DA DALILIN KARBAR
TUTA DA YADDA SUKA TUNKUDE SARAKUNAN
HABE DAGA SARAUTA.

THE ORIGIN OF FULANI (Asalin Fulani)


Who Are the Fulani People? Origins The
history of the Fulani seems to begin with the
Berber people of North Africa around the
8th or 11th century AD. As the Berbers
migrated down from North Africa and
mixed with the peoples in the Senegal
region of West Africa the Fulani people came
into existence. Over a thousand year period
from AD 900 - 1900, they spread out over
most of West Africa and even into some
areas of Central Africa. Some groups of
Fulani have been found as far as the
western borders of Ethiopia. As they
migrated eastward they came into contact
with different African tribes. As they
encountered these other peoples, they
conquered the less powerful tribes. Along
the way many Fulani completely or partially
abandoned their traditional nomadic life in
favor of a sedentary existence in towns or
on farms among the conquered peoples.
The nomadic Fulani continued eastward in
search of the best grazing land for their
cattle. Their lives revolved around and were
dedicated to their herds. The more cattle a
man owned, the more respect he was given.
Today, some estimate as many as 18 million
Fulani people stretch across the countries of
West Africa. They remain to be the largest
group of nomadic people in the world. What
Do the Fulani Believe? Religion and Beliefs:
The Fulani were one of the first African
tribes to convert to Islam and are today
more than 99% Muslim. The devoutly Muslim
Fulani have seen themselves as the
propagators and preservers of the Islamic
faith in West Africa from as early as the
fourteenth century. Historically it was a
Fulani chief named Usuman dan Fodio,
along with nomadic Fulani herdsmen who
were instrumental in facilitating the spread
of Islam across West Africa through
evangelism and conquest. At times they
would wage "holy wars" or jihad in order to
extend and purify Islam. As the Fulani
migrated eastward they spread their Islamic
beliefs. As they became more powerful and
attained more wealth they began to be
more aggressive with their religion. Their
adoption of Islam increased their feeling of
cultural and religious superiority to
surrounding peoples, and that adoption
became a major ethnic boundary marker.
Some settled in towns and quickly became
noted as outstanding Islamic clerics, joining
the highest ranking Berbers and Arabs.

Sunday, July 8, 2012

WAKAR SAUDATU ADO BAYERO



1, Daren jiya ba na yau bane gun kwanan
yaro daban da bubba.



2, Bismillah zana shirya waka sarki Allah
kaban basira inyi wakar saude 'yar nikatau.



3, Ina dada godiya ga Allah sarkinda ya halicci saude.



4, Ga saude sarauniyar kano mai saukin kayi da son mutane.



5,Ga mai fara'a da son mutane Bata gaji tsiya da tsangwama ba.


6, A wajen kyauta fa ba kamar saude 'yar
sarkin kano na korau.



7,Ga mai haske kamar Azurfa Dadin suna kamar Tagullah.


8,Taurari ko suna da haske basu kai hasken farin wata ba.



6, Inda mata suna sarauta a kano mukan
muna da saude.



7, A zaria sunyi Quen Amina muma a kano muna da saude.



8, A gabas na dangana da Borno ba
kyakkyawa kamarki saude.



9, A yamma najeni har Ilorin ni banga ba
wadda tayi saude.



10, ta nan kudu har zuwa Adamawa banga ba wadda tayi saude.



11, A arewa saida na wuce Nijar banga ba
wadda tayi saude.



12, Kai duk matan dake cikin facebook babu wadda tayi saude.



14, Hotonki ana comment akanshi na kirga Comment dubu a yanzu.



15, Ga allurar cikin duhu sai mai zurfin
hankali ka tsinta.



16, Ga saude bakin zare a matoya sai mai
hankali ka tsinta.



17, Ni burina a duniya inga kina mulkin
kano sa'ade.



18, Allah ba yanda bai iya ba a zazzau shi ya bai Amina.



19, Ansa giwa cikin zubo taci guda bakin
rabonta kelau.




20, Allah in yai nufi ga iko nai babu abinda
zai hana shi.

Friday, July 6, 2012

THE ESTABLISHMENT OF SOME OF THE OLD SETTLEMENTS IN HADEJIA EMIRATE


HADEJIA A YAU!
We are severely constrained in the producing a coherent, meaningful and definite pattern of the process of the evolution of Hadejia emirate due to the limitation by our main source-oral tradition. Most of the traditions collected hardly touch on the process of the evolution of Kasar Hadejia. But in spite of this difficulty, we intend to take a second look at the source through a new-interpretation in the hope of coming out with a better understanding of the process of the evolution of Hadejia emirate. Towards this end, we shall attempt to discuss the process of the evolution of certain Old settlement in the emirate, with a view to paving way towards grasping the process of the evolution of Kasar Hadejia as whole.

Prior to the jihadist conquest at the beginning of the 19th century, the territory now known as Hadejia emirate consisted of several separate and distinct Kingdoms whose rulers received titles from and owed allegiance to the Habe Galadima of Borno.

The former Habe Kingdoms included Auyo,Garin Gabas(Biram),Hadejia,Kazura,Gaturwa,Marma,Dawa and Fagi. The process of the evolution of these Kingdoms of seems to be obscure except perhaps for the Kingdoms of Hadejia,Auyo and Garin Gabas.

At the time of the foundation of Hadejia,a number of small settlements were said to have existed in the territory that came to be known as Hadejia emirate. For example,on the North-eastern side of Hadejia town, there was Madagwaigwai, whose present site is near Rubban Dakata a village about 10kilometres east of Hadejia Kiri kasamma road. While on the eastern side of the town was Maskangayu (kulunfardu), a village said to have been established by Damagarawa immigrants whose ancestors now live in Hadejia (ILALLAH).

The old site of Kulunfardu was located near Tandanu, just by the valley of River Hadejia, about 15kilometres from TURABU.
There was a tradition in Turabu which said that, at the side of kulunfardu, there was a large Tamarind (Tsamiyar linzamai) whose branches were said to have bent due to the weight of the Luggage of soldiers of Mai Ali of Borno when they camped there on their way to attack Kano during the reign of Sarkin Kano Muhammadu Kambari Dan shariff(1731-1734) By the western side of Hade's camp was KADIME (still located to the site) which was about 9kilometre from Hadejia. By the Northern side of Hadejia was Majeri a few kilometre from Mallam madori, and by the southern side were Auyakayi(Tunawa), Unik(Arki), Majawa and Auyo.

These settlement were clearly established in the surrounding areas much earlier than Hadejia town.
End of page One.
A short History of Hadejia 1800-1906. By Musa Usman Mustapha.
Ana saida shi a k.liman.

Thursday, July 5, 2012

SARKIN HADEJIA BUHARI DA WAZIRIN SOKOTO A KATAGUM


HADEJIA A YAU! Wannan Bindigar Sarkin Hadejia Buhari ce. A lokacinda Sarkin Musulmi Aliyu Bubba ya turo Wazirin Sokoto Abdulkadir Gidado Gurin Sarkin Hadejia Buhari, Wazirin Sokoto shine wakilin sarkin Musulmi a yankin Gabas sai ya taho Hadejia daga Kano Amma sai ya wuce Katagum, Ya turo Jakada zuwa Hadejia yana So su Gana da Sarki Buhari. Buhari yayi tunanin ya tafi shi kadai daga baya sai ya canza shawara kawai ya Tafi Katagum Da Mutanensa. zasu gamu da Wazirin Sokoto a can. Lokacinda suka isa Katagum Sarkin Hadejia Buhari ya tsaya a Kofar Garin Katagum sai ya tura a fadawa Waziri Ya Iso Wazirin Sokoto da Sarkin Katagum suka zo sai sukace Buhari ya Biyosu amma shi kadai tunda Shawara zasuyi. Sarki Buhari ya bisu Har ya shiga Kofar Garin Katagum. Sai Mawakinsa wato DAN FATIMA ya fara masa waka yana cewa:-

1, Abubakar Garba Mijin Maza,

2, Buhari kai ke da Nutso Kai ke da Hankali.

3, Don Allah yayi ka Uban Jama'a

4, Kuma kai Allah ya baiwa shugabancin Gidan Sambo

5, Ba dan na isa ba, In ka yarda ga Aike ka shiga dashi

6, Fasa Maza Gagara gasa Aiken shine

7, In ka sauka lafiya ka gaida Na Lara Sarkin Auyo

8, Ka gaida Bello Sarkin Dutse

9, Na Sambo sai ka dawo.

Abinda Dan fatima yake Nufi Sarkin Auyo da Sarkin Dutse duk Buhari ya kashe su. Dan haka shima In ya shiga Katagum Lalle Bazai fito ba. KodaSarki Buhari yaji Wannan Waka ta Dan fatima sai ya juyo da baya, Wazirin sokoto da Sarkin Katagum da suka fahimci Buhari ya juya sai suka Biyoshi da Ihu Su da mutanen Katagum Suna ce masa Kafiri yaki bin Umarnin Sarkin Musulmi. sai da suka biyoshi har Unik Iyakar Hadejia Da Katagum. kuma sun kashe wasu daga mutanen Buhari. koda yazo Unik sai ya yanke Shawarar ya yi sansani a nan ya koma ya yaki Katagum. kuma mutanensa suka koma suka Karkashe Mutanen Katagum karkashin jagorancin Barde Risku. Daga nan Rashin Jituwa Tsakanin Hadejia da Katagum ya Fara har bayan shekara Goma sha biyu bayan Mutuwar Buhari. ((1863). daga nan Aka samu wasa tsakanin Hadejia da Katagum. koda Katagumawa suka juya sai Wazirin Sokoto ya sake Gyyato Mutanen kano suka Hadu da Na Katagum zasuzo su yaki Buhari. da sarki Buhari yaji wannan Labarin sai shi da mutanensa suka bar Hadejia suka tafi Shabawa Iyakar Hadejia da Gumel Sukayi sansani a can. da Buhari ya bar Hadejia sai Wazirin sokoto ya nada Wansa Ahmadu Sarkin Hadejia. A shekarar (1850).Wanda dama saboda shi suka Takurawa Sarki buhari.

SARKIN HADEJIA BUHARI DA WAZIRIN SOKOTO A KATAGUM KASHI NA (2)

Image Hosted by ImageTitan.com HADEJIA A YAU!

A kashi na farko kunji yanda Buhari suka kare da Wazirin sokoto da Mutanen Katagum: da kuma komawar sarki Buhari shabawa wato iyakar Hadejia da Gumel da kuma Damagaram.

YAKIN TAKOKO:- Bayan an Nada Ahmadu a matsayin Sarkin Hadejia, sauran Magoya bayan Buhari sai suma suka bar Hadejia suka koma Shafowa inda Buhari yake suka zauna tare. Sarkin Hadejia Buhari anan ya zauna tsakanin Takoko da Shafowa a Arewacin Hadejia da mutanensa kuma yake tafiyar da wannan yankin. Kuma iyakar Hadejia ce da Damagaram da Machina ta Arewa maso Gabas wato yankin Niger da kuma Borno. Kuma Buhari ya bada Gudun mawa sosai a wannan Yankin wajen Maidasu Musulmi. Inda yayi ta jihadinsa a yankin, kuma a wannan zama da yayi a Shafowa Buhari ya samu kyakkyawar dangantaka da Sarkin Machina da kuma Shehun Borno Umar wanda ya mulki Borno a wannan shekara (1835-1880) wannan dangantaka ta kara baiwa Buhari karfin gwiwa.


A shekarar 1851, Sarkin Musulmi Alu Bubba ya yanke shawarar daukan matakin Karshe akan Buhari, saboda yana tunanin Shehun Borno zaiyi amfani da Buhari ya rusa Daular Sokoto saboda ya zame musu Barazana a Arewa Maso Gabas. A wannan lokacin kuma DanGaladiman Sokoto ya hada Mayaka daga Hadejia,Kano,Katagum,Misau da Jama'are zuwa shafowa.

A wannan lokacin kuma Buhari ya fita kudu da shafowa shi da Sarkin Machina yana garin Takoko shida Jarumansa. A lokacinda Dangaladiman sokoto suka fito su yaki Buhari sai ya zabi Sarkin Jama'are Samboli ya jagoranci yakin, saboda shi ya fisu sanin Yankin. A ranar da zasu yaki buhari kuma a ranar Buhari ya shirya mamaye Garuruwanda suke kudu da Hadejia, sai aka hadu a Garin Takoko. Yayin da aka hadu aka gwabza fada Buhari yaci Galaba a kansu duk suka gudu, Sarkin Hadejia Ahmadu yayi kokarin ya Gudu Kasar Kano amma sai Barde Risku ya bishi ya Kashe shi.

Bayan Yakin Takoko yazo karshe kuma an kashe Sarkin Hadejia Ahmadu Amma ba'a son ran Buhari ba kuma aka masa Sallah aka kaishi Hadejia aka binne shi, sannan sai Buhari ya koma Hadejia yaci gaba da Mulki. Sakamakon wannan yakin, dangantaka ta sake baci tsakanin Hadejia da Sokoto, kuma Sarkin Musulmi yaki yarda da ya nada Buhari Sarkin Hadejia. Sai ya nada Tukur Na yayari, kanin Sarki Ahmadu kuma yace ya zauna a Mashama a Kasar Katagum a Matsayin sarkin Hadejia ya Gaji wansa Ahmadu. Amma Tukur bai yarda ya zama Sarkin Hadejia ba saboda yana tsoron Buhari, sai yaga bazai iya yin haka ba. Kuma saboda Gudun kar Buhari ya kasheshi sai Tukur ya Gudu daga Mashema yayi kaura zuwa Kano Lokacin Sarkin Kano Usman Na1(1846-1855) Sai aka Turashi ya Mulki Yayari a Kasar Birnin Kudu. (Yayarin Tukur) Tukur ya zauna acan Har zuwa lokacinda ya Mutu 1909. Buhari kuma yaci gaba da mulkin Hadejia yana kai hare hare a matsayin Jihadi Har saida yakai Gabasawa,Sankara,Ringim da Kuka kwance A Arewa maso yamma. A Kudu saida ya mamaye Kununu,Takalafiya, Kafin baka, Doma, Ruba, Itas da Kwanda. A Gabas kuwa saida ya Mamaye Babuwari, Kazura, Dawah, Gatare da Margadu. Saida Sarki Buhari ya fadada kasar Hadejia tafi Ko ina fadin Kasa a karni na19.

GAMON KAFUR:-

Tuesday, July 3, 2012

DAJIN DUHUN KARO A HADEJIA.



HADEJIA A YAU! DUHUN KARO:-duhun karo wani Daji ne dake kasar Hadejia ko ince Gabas da Hadejia. Kuma daji ne mai Dimbin tarihi wanda duk wanda yake kasar Hadejia zaice maka haka ya taso yaga wannan Dajin. Kuma yana tafe ne da Ruwa a Gefensa. Kuma wannan dajin ya taso ne tun daga Falgore har ya dangana da komadugu ta Jihar yobe. Duk wanda ya saba bin hanyar kano ta Ringim zai ga wannan dajin musamman kwanar Auyo zuwa Hadin mai dan karofi inda nan ne ya fito bakin titi.
Na shiga wannan Dajin kuma banda kukan tsuntsaye da Namun daji babu abinda kake ji. Nayi tafiyar kilo meter takai biyar a cikin dajin, na gamu da wani Bafulatani mai suna Musa kuma na tambayeshi shekarar sa nawa a wannan dajin? Sai yace shima anan aka haifeshi kuma yanzu shima yana da 'ya'ya wadanda ya haifa anan. Na tambayeshi ko zai bani labarin wannan dajin? Sai yace ya tashi yaga Kuraye suna zuwa suna razana musu shanu, kuma yace akwai Namun daji kamar Gada,Barewa,Bauna da sauransu. Amma tunda aka fara sarewa dajin sai sukayi nisa kuma da 'yan farauta da suka damesu. Yace Amma har yanzu akwai kananan Namun daji kamar Zomo, Guza, kuma wani lokacin ana samun Gada. Tsuntsaye kuwa dukda harbi da ake Har yanzu akwaisu da dama.
Dajin in ka shiga cikinsa baza kasan ana rana ba saboda tsabar Inuwa da take ciki kuma ga Ruwa a gefensa. Akasarin bishiyoyin da ke dajin farar kaya ce da kuma Bishiyoyi kamar su Danya,Darbejiya,Kirya,Kanya,Magarya, da sauran bishiyoyi masu Ni'ima.
Kalu balenda wannan Daji yake fuskanta shine Sare saren Bishiyoyi da ake yi a cikinsa da kuma fadada Gonakai da makwaftan dajin sukeyi. Ta wani fannin kuma akan samun wasu suna kunna masa wuta. Amma dukda haka in ka shiga zai baka sha'awa. Na tambayi wani dattijo mai suna Garba Tandanu mai shekara 60, yace wannan dajin yasan lokacin da kuraye suke Hanasu zuwa Hadejia ta Rugar Isa inda sai sun zagaya ta Tuwankalta sannan zasuzo Hadejia Amma yanzu sai dai tsuntsaye da kananan namun daji. HADEJIA A YAU.

Sunday, July 1, 2012

KASAR HADEJIA ZAMANIN SARKI ADAMU




HADEJIA A YAU! Hadejia tana daya daga cikin Garuruwan da ke Karkashin Tutar shehu Usman Danfodiyo! Jama'ar Hadejia Akasarinsu fulani ne da Hausawa da Mangawa. Kuma Suna bin Addinin Musulunci ne. Idan muka tabo Tarihin Hadejia tun lokacin mulkin Habe zamuga cewa dama ko a wancan lokacin Addinin Musulunci ne addinin mutanen Hadejia sai dai dan abinda ba'a rasa ba. Kafin a jaddada addinin Musulunci lokacin shehu dan fodiyo sarakunan Habe ne suke Sarautar Hadejia, kuma anyi sarakuna da dama kamar (1)Baude(2)Musa(3)Abubakar. Bayan Malam Sambo ya karbo tuta karkashin jagorancin Sarkin fulani Umaru sai Hadejia ta koma Karkashin mulkin Fulani.
HADEJIA A YAU! A yau Hadejia ta zama wata fuskar kasuwanci a jihar Jigawa, domin duk abinda ka sani na sayarwa zaka samu a wannan gari. A shekaru Hamsin baya In ba ranar Kasuwar Garin ba wani abin bazaka samu ba. Allah ya albarkaci Hadejia da kayan Lambu Irinsu Tumatir, Tattasai, Attaruhu, da sauransu. Wadannan ana yinsu ko wane lokaci a Hadejia ba sai da damana ba. Saboda Albarkar kogi da Allah ya bamu. Haka kuma fannin kayan Abinci kamar shinkafa,Alkama,Masara. Duk ba sai da damina akeyinsu ba a Hadejia. Saboda Albarkar da Allah ya bamu ta kasar Noma mai kyau. Idan muka koma batun Amfanin Abinda ke cikin Ruwa Hadejia A kullum Tana Fidda kifi kimanin Na Naira milyan Biyu a takaice! Wani abu da yake shine Kalu bale a garemu shine.........

Saturday, June 30, 2012

GWAMNATIN JAR HULA. SAI KANO


HADEJIA A YAU! Tarihi shike maimaita kansa! Kamar yanda aka sani a da can mun san wasu dattijai wadanda kullum Adonsu shine: farar riga bakin takalmi da Jar hula. Bamu sani ba ashe adon nasu yana da fa'ida, ba wai suna yi bane dan kansu. A lokacin jamhuriya ta daya anyi jam'iyyun siyasa da dama a cikinsu har da NEPU. Kuma kowace jam'iyya tana da nata taken kuma tana da Tuta Irin tata. To ashe wannan adon da mukaga wasu daga cikin Dattijanmu sunayi ado ne mai ma'ana saboda suna cikin jam'iyyar NEPU. Kuma sun saka akidarta a ransu shi yasa suka maida adonsu irin na tutar jam'iyyarsu. Haka ma a jamhuriya ta biyu anyi jam'iyyu da dama a ciki harda P.R.P. Kuma su 'yan jam'iyyar NEPU sune suka kafa P.R.P. Dan haka sai suka sake saka alamarsu ta da can ta zama itace dai alamar P.R.P.
KWANKWASIYYA!
A shekarar 2011 Kano ta sake maimaita wannan tarihi karkashin Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso Inda ya dawo da wancan adon na 'Yan NEPU. Shima ya maida adonsa farar riga da Jar hula kuma hakan ya samu karbuwa ga jama'ar kano. Yanzu farin yadi da jar hula kasuwarsu tafi garawa ba wai kano kadai ba harda jigawa da Bauchi da Kaduna da Katsina. Sai dai da yawa masu saka Jar hula in ka tambayesu basu san Ma'anar Hakanba. Kawai dai sunga Kwankwaso yana sakawa.

Wednesday, June 27, 2012

KANO GARIN ALHERI.


HADEJIA A YAU! Kano ba gari ba Dajin Allah Inji masu iya magana! Tarihin kano abu ne wanda sai dai ace an baka kadan daga cikinsa, domin tarihinta bazai kammalu ba ga duk mai rubuta shi. An kafa kano tun a farkon karni na biyar bayan haihuwar Annabi Isah (AS) wato 500AD. Idan akayi la'akari da zuwan Bagauda da mutanensa. Tun daga wannan lokacin ake mulkin kano kawo yanzu mulkin fulani.
Kano ta shahara ta fannoni daban daban kama daga Ilmin Addini da na boko da kuma Uwa uba kasuwanci wanda ta zama babu kamarta a duk jihar Arewa. Al'adunsu da dabi'unsu abin koyi ne ga duk wanda yayi mu'amala dasu. Allah ya albarkaci kano da Ni'imomi daban daban wadanda basu misaltuwa. Kasuwa kuwa duk abinda ka sani ana sayarwa a duniya zaka samu a Kano, kuma duk abinda kake sayarwa zaka samu masu saye.
Kano ta zama wata cibiya ce wanda duk abinda ya sameta lalle ya samu duk jihar Arewa baki daya. A watannin baya ne kano ta samu kanta a wani hali wanda bata taba zatonsa ba. Wato na hare haren bom da kashe kashen jama'a wanda hakan ya kawo cikas a al'amuran yau da kullum. Amma duk da haka ba'a fasa saye ana sayarwa ba kamar yanda aka saba. Lalle duk abinda ya taba hanci to idanu zaiyi ruwa! Wato duk abinda ya taba kano to hakika ya taba Arewacin Nigeria.
Jama'ar kano da ma Arewacin Nigeria... Na rigingine fa ba-a fada masa ganin farin wata. Ina nufin mun san gurin wanda zamu kai kukan mu, shine sarkin da ya kafa kano ya albarkaceta da mutane Irin su WAZIRIN KANO, Da sauransu. Muna rokon Allah ya karemu daga duk abinda zai kawo barazana ga Kano da ma Arewacin Nigeria. Allah ka mana maganin abinda yafi karfinmu da abinda bamu zaton sa. Domin da ikonsa ne komai ya kasance da kuma abinda zai kasance. KANO KWARYAR KIRA MATATTARAR ALKAIRI. Daukar Nauyi freedom Radio kano.

TARIHIN SARAUTAR SARKIN HADEJIA NA (16)

Image Hosted by ImageTitan.com

Sarkin Hadejia, Zan baku Tarihin Sarautar sa
zuwa Yau!
Ranar Asabat 3-january-1999, Mai martaba
sarkin Hadejia Alh. Abubakar Maje Haruna ya
Nada Alh. Adamu Abubakar A matsayin IYAN
HADEJIA, NA FARKO. Kuma Ranar Laraba 11-
september-2002, Allah ya yiwa Mai martaba
Sarkin Hadejia Rasuwa. Alh. Abubakar maje
Haruna.
TO A SAKAMAKON AMINCEWA DA GWAMNATI
TAYI DA ZABEN 'YAN MAJALISSAR SARKI WATO
(KING MAKER'S) Suka zabi Iyan Hadejia Alh.
Adamu Abubakar maje a matsayin sarkin
Hadejia, Na Goma sha shida (16). kuma an
nada shi Ranar Asabat
14-september-2002. Bisa Al'ada ba'a kwana
uku ba tare da an nada Sarki ba.
KUMA HAWANSA NA FARKO A MATSAYINSA NA
SARKIN HADEJIA SHINE Hawan sallar Azumi
wato A watan Disamba 2002. Sannan sallar
Layya February 2002 Bai Hau ba saboda yaje
Saudiyya.
29-March-2003.
A YAU ASABAT 29-March-2003 ANYI BIKIN
BADA SANDA! An baiwa sarkin Hadejia Sanda
a Karkashin shugabancin Gwamnan Jigawa
ALH. IBRAHIM SAMINU TURAKI! A STADIUM TA
HADEJIA.
Kuma bayan an Bashi Sandar jagorancin
Kasar Hadejia A karkashin Tutar Shehu
Usman Dan fodio, Mai martaba sarki yayi
Hawa Guda Uku Wadanda suka Kayatar da
jama'ar Hadejia.
1, BIKIN GASAR ALQUR'ANI A SECONDARY
FANTAI
2,TARON DA AKAYI A MAKARANTAR KOFAR
AREWA
3,SAI HAWAN GANDU WANDA SHIMA YANA DA
TARIHI A MASARAUTAR HADEJIA.
Kuma Hakiman da ya fara Nadawa sune 1,
DAN GALADIMA Alh.babbaji Adamu Hakimin
waje 2, SARKIN DAWAKI Alh. Umar Ibrahim
Hakimin kiri kasamma.
3, KATUKAN HADEJIA NA (2) BIYU Hakimin
Turabu. A gaba zan kawo muku Labarin
Fitar sarkin Hadejia Rangadi da yayi da kuma
Hakiman da a Nada.

Tuesday, June 26, 2012

RABE DA MUTANEN BORNO


HADEJIA A YAU!
Baramusa wani kauye ne a karamar hukumar Birniwa! Naje ziyara kauyen kuma ganin cewa duk barebari ne a garin, sai na samu damar in tambayi tarihin Rabe dan Fataralle. Na samu wani dattijo mai shekara 76, sai na tambayeshi tarihin Rabe. Kafin ya bani amsa saida ya tsinewa Rabe.
Yace wani mutumin sudan ne wanda ya Addabi bare bari tun daga kukawa Har zuwa Bedde. Sannan yace Rabe ne dalilin zuwansu nan kuma yace duk Babarbare ko bamangenda naganshi a Kasar Hadejia ko wani Guri, to lokacin Rabe ne suka Gudo nan. Yace kamar Kacallari,Kaigamari,kuka Ingiwa,Birniwa.kirikasamma,Jibori, da sauransu duk Gudun Rabe sukayi. A lokacinda Rabe yaje kukawa ya kashe duk mutanen Garin wasu da suka samu labari sai sukayi gudun hijira kasar Hadejia. Wasu kuma suka shigo cikin Hadejia kamar Gagulmari,Kakaburi,zonagalari,kilabakori da sauransu. Yace da can suna da zanen barebari amma yanzu sun canza sai suke zanen a kan fuskarsu wato uku uku. Sauran Labarin sai a Gaba.

Monday, June 25, 2012

GARKO DA SANA'AR SU. TUN KAFIN ZUWAN BATURE


HADEJIA A YAU! GARKKO Unguwar Garko Tana daya daga cikin unguwannin da suke Garin Hadejia, kuma Unguwa ce mai dimbin tarihi idan mukayi La'akari da Dadewarta. Garko tana daya daga cikin garuruwanda sarakunan Habe suka mulka a Hadejia amma A lokacin Gari ne mai zaman kansa kafin ya hade da Hadejia ya zama Unguwa. Kuma suna da sana'ar su wanda suka gada Iyaye da kakanni. Hakan ta bunkasa tattalin Arzikinsu tun a wancan lokacin zuwa yanzu. Sana'ar su Itace Amfani da kasa ko yumbu domin yin Randa,Gajirami,Tukunya,Tuli,Kula,Kasko,kafara da dai sauransu. Kuma wadannan kayan sune kayan da ake amfani dasu a kasar Hausa kafin zuwan Turawa. Domin Amfanin Gida wato Girki ko Aje ruwa ko makamantansu. Na samu wani Dattijo yana gina Randa a kofar gidansa Na tambayeshi ko A ina suke samun yumbun da suke gina randa? Yace duk a Hadejia suke samu akwai Mailolo ta Gabas da Hadejia anan suke samo yumbun da suke gina duk abinda nagani anan. Na tambayeshi ko shekara nawa yana yin wannan sana'a? Sai yace ya kai shekara Hamsin da biyu yana yi, kuma suna yi ne da Mahaifinsa da kannensa har zuwa yanzu ya zamanto shine bubba. Na tambayeshi menene dalilin da in an gina ake zuwa a gasa ta a wuta? Zan kawo muku karashen firar mu.

Saturday, June 23, 2012

JUMA'A RANAR ALKAIRI


Ranar jumaa itace mafi alherin dukkan wata
rana da rana ta fito a cikinta. cikinta Allah ya
halicci Adam, cikinta ne qiyama zata tsayu,
kuma ita ranar idi ice ga musulmai.Don haka
nema aka sharanta wasu abubuwa acikinta,
daga ciki akwai: hudubar jumaa, wanka,
fesa tirare, fita cikinta da mafi kyawun kaya
da yanayi me kyau, yin kabarbari lokacin fita
sallar, kusantar liman, da kuma tara tunani
gaba daya domin sauraren wa'azi da
ambato (wato huduba).

Friday, June 22, 2012

TARIHIN RAYUWAR SHEIKH JA'AFAR M. ADAM


An haifi marigayi Sheikh
Ja'afar Mahmoud Adam a
garin Daura, a shekara ta 1962
(ko da yake wani lokacin
yakan ce 1964).
Marigayi Sheikh Ja'afar ya fara
karatunsa na allo a gidansu, a
wurin mijin yayarsa, Malam
Haruna, wanda kuma dan
uwansu ne na jini. Daga nan
kuma sai aka mayar da shi
wajen wani Malam Umaru a
wani gari wai shi Koza,
kimanin kilomita 9 a arewa da
Daura, wanda shi ma akwai
dangantaka ta jini a tsakanin
su, wanda kuma shi ne
musabbabin zuwansa Kano.
Bayan sun zo Kano ne tare da
wannan malami nasa, a
shekara ta 1971 (ko 1972), sai
suka zauna a makarantar
Malam Abdullahi, wanda
asalinsa mutumin jamhuriyar
Nijar ne, amma yake zaune a
unguwar Fagge a Kano. Tun
kafin zuwansu Kano, tuni
marigayi Sheikh Ja'afar ya riga
ya fara haddar Alkur'ani mai
girma, wanda ya kammala a
shekara ta 1978.
Bayan da Malam ya kammala
haddar Alkur'ani mai girma,
kasancewarsa mai sha'awar
ilimi, sai ya shiga makarantu
biyu a lokaci daya a shekara
ta 1980. Ya shiga makarantar
koyon Larabci ta mutanen
kasar Misra a cibiyar yada
al'adun kasar Misra, (Egyptian
Cultural Centre), sannan
kuma ya shiga makarantar
manya da ba su yi boko ba ta
Masallaci Adult Evening
Classes, tunda a lokacin
shekarunsa sun wuce shekaru
na primary, amma duk da
haka a wannan lokaci shi ne
mafi kankanta a ajinsu. Haka
ya rika yin wannan karatu
guda biyu: Waccan
makarantar ya je ta da
daddare bayan sallar isha'i,
waccan kuma ta koyo harshen
larabcin da yamma. Ya
kammala wadannan
makarantu a shekara ta 1983.
Wannan kuma shi ya ba shi
damar shiga makarantar
GATC Gwale a shekara ta
1984, kuma ya kammala a
shekara ta 1988. A shekara ta
1989, malam ya sami gurbin
karatu a jami'ar musulunci ta
Madinah, a inda ya karanta
ilimin tafsiri da Ulumul Kur'an,
wanda kuma ya kammala a
shekara ta 1993. Sannan kuma
Sheikh Ja’afar ya sami damar
kammala karatunsa na digiri
na biyu (Masters) a Jami’ar
Musulunci, A Oundurman Sudan.
Sannan kuma, kafin
rasuwarsa, ya riga ya yi nisa
wajen karatunsa na digiri na
uku, wato digiri da digirgir
(PhD), a Jami’ar Usman Dan
Fodiyo da take Sokoto.
Daga cikin malamansa na
ilimi, akwai malaminsa na
farko, mutumin kasar Masar,
Sheikh Abdul-Aziz Ali al-
Mustafa, da kuma Malam
Nuhu a unguwar Dandago,
wanda malam ya karanci ilimi
fikihun malikiyya da wadansu
littattafai na hadisi a gurinsa,
da kuma Malam Muhammad
Shehu, mutumin Lokoja,
wanda Malam ya karanci
nahawu da sarfu da balaga da
adab a wajensa. Akwai kuma
Sheikh Abubakar Jibrin
limamin masallacin Juma'a na
BUK, akwai kuma Dr. Ahmad
Muhammad Ibrahim shi ma na
jami'ar Bayero ta Kano. Daga
cikin malamansa na jami'a
kuma, akwai Sheikh
Abdurrafi'u da Dr. Khalid
Assabt.
Daga cikin karatuttukan da
malam ya karantar da su, sun
hada da tafsirin Alkur'ani mai
girma, Kitabuttauhiid,
Umdatul Ahkaam, Arba'una
Hadiith, Kashfusshubuhaat,
Bulugul Maraam,
Riyaadussalihiin, Siiratun
Nabawiy, Ahkaamul Janaa'iz,
Siffatus Salaatun Nabiiy.
Wasu daga cikin daliban
malam sun hada da Malam
Rabi'u Umar R/Lemo da
Malam Sani Abdullahi
Alhamidi Dorayi da Malam
Abdullah Usman G/Kaya da
Malam Usman Sani Haruna da
Malam Ibrahim Abdullahi Sani
da Malam Ali Yunus
Muhammad da Dr. Salisu
Shehu da Malam Shehu
Hamisu Kura da Malam Anas
Muhammad Madabo.
Kafin rasuwarsa, malam ya
fara gagarumin aikin rubuce
tafsirinsa a harshen Hausa a
karkashin wannan cibiya
(Sheikh Ja'afar Islamic
Documentation Centre).
Marigayi Sheikh Ja'afar
Mahmoud Adam ya rasu ranar
juma'a 26/Rabii'u Awwal/1428
(13/04/2007) sakamakon harin
da wadansu 'yan ta'adda suka
kai masa, a daidai lokacin da
yake jagorantar sallar asuba a
masallacin Juma'a na Dorayi.
Ya rasu ya bar mata biyu, da
'yaya shida, yayin da aka haifa
masa ta bakwai kwanaki 58
daidai bayan aiwatar da
wannan kisan gilla a kansa.
Dubun-dubatar mutane ne
daga ko'ina cikin kasar nan
suka halarci jana'izarsa, kuma
an binne shi ne a makabartar
Dorayi. Allah ya ji kan sa ya
gafarta masa, ya saka masa
da gidan aljanna. Amin

Thursday, June 21, 2012

SAKO ZUWA GA MASU AMFANI DA FACEBOOK


Malam Yusuf Audi, ya
rubuta cewa kamar haka...
Shafukan INTERNET da
Wayar hannu ta
GSM...... Bincike ya nuna
cewa shafin internet na
FACEBOOK da wayar hannu
ta GSM suna
daga cikin ababen dake
kara rura wutar
fadan addini a Nigeria.
Hakan yana faruwa
sakamakon irin yadda
mutane ke amfani da su
wajen isar da
sako atsakanin su.
Mutanen mu suna da son
bayar da labari,
ingantacce ko mara
inganci don neman
addu'ar 'yan uwansu ko
don nuna bajintar
su ko kuma don wata
manufa ta su ta
daban. Wannan yasa
dayawa sukan fidi abin da
ba
su da tabbas akan shi, ko
kuma suyi kari
cikin labarin na su. Ya kai
dan uwana me son bayar
da labari!
Kaji tsoron Allah, kada
kafadi, kada
karubuta sai abin da kaji
ko kagani ko
kuma kake da tabbas akan
shi. kasani za ka amsa
tamyar Allah akan abin
da kake fadi ko kuma kake
rubutawa
duniya(facebook), wacce
amsa katanada?
Ba wani abin birgewa
bane afara jin
labarin dake tayar da
hankali agurinka. Na ji
ance sun ce, wannan ba
dalili bane.
Addinin muslunci ya hore
mu da yin
magana ba tare da ILIMI
ba. Mu kiyaye ko Allah
(S.W.A) ya kiyaye mu. Ya
Allah! Kakiyaye mu,
kabamu zaman
lafia, amin.
To Jama'a sai mu kula da
fadar jita jita, domin karya
haramun ce. Allah ya kare
mu ameeeeeeeeen