Thursday, March 20, 2014

TARIHIN SARAKUNAN FULANIN HADEJIA (Kashi na daya 1)

TARIHIN SARAKUNAN FULANI A HADEJIA...



BISMILLAHIRRAHMANIR'RAHIM.

. Kamar yanda aka sani kasar Hadejia ta koma karkashin mulkin fulani bayan da suka hambarar da mulkin Habawa a karni na goma sha biyar (15). Fulani sun shigo kasar Hadejia ne a farkon karni na goma sha biyar (15), a karkashin jagorancin Ardo Abdure dan Jamdoyji, sun fara zama ne a Jarmari kusa da garin Hadejia, har tsawon wani lokaci. Bayan rasuwar Ardo Abdure a shekarar (1788) sai Dansa Sarkin fulani Umaru ya yanke shawarar su dawo Rinde da zama, yamma da garin Hadejia. kuma Sarkin Hadejia na Habe Abubakar ya nada Umaru a matsayin Sarkin fulanin Hadejia a cikin karni na goma sha takwas (18).

SARKIN FULANI UMARU... Shine sarki na farko a jerin sarakunan fulanin Hadejia, kuma a lokacinsa aka samu labarin jihadin Shehu Usman Danfodiyo. A lokacinda sarkin fulani Umaru yaji labarin jihadin shehu sai yayi shawara da 'yan uwansa da suje suyi Mubaya'a da Da'awar Shehu. Sai ya tashi dan uwansa Sambo yaje ya meka mubaya'arsu ga Shehu da kuma nuna goyon baya ga da'awarsa ta Addinin musulunci.Sambo ya kai chaffarsa ga Shehu a cikin shekarar 1807-1808. A wannan shekara ne jama'a daga garuruwa daban daban sukayi mubaya'a ga shehu, musamman Fulani wadda sune suka taimaka masa wajen jaddada Addinin Musulunci a kasar Hausa.

Bayanda Umaru ya tura Sambo zuwa ga Shehu, sambo ya tafi da  kaninsa Laraima da kuma sauran fulani 'yan uwansa. Shehu ya zabi Sambo da ya zama shine shugaban jaddada jihadi a kasar Hadejia saboda dama Sambo yana daga Dalibansa. Bayan sun dawo Hadejia sukaci gaba da jaddada Addinin Musulunci a ciki da wajen kasar Hadejia.kuma dukda basu samu turjiya da yawa a cikin garin Hadejia ba, Sarkin fulani Umaru da magoya bayansa sun samu turjiya da yawa musamman a yankin Gabas iyakar Hadejia da Nguru da kuma yankin Auyo. Fulanin Hadejia sun fara jaddada jihadinsu ne a Wajen Hadejia, inda suka fara da kauyukan da suke kusa da Rinde kamarsu Akurya da kadime da sauransu


Monday, March 17, 2014

JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO (DAGA NA GABA PART FIVE 5)

TAKAITACCE TARIHIN MAIGIRMA JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO!!

Daga Muhammad Yawale.


An haifi Alh. Abba sambo a shekara ta 1943 a cikin garin hadejia, ya fara karatun allo a matakin karatunsa na farko sannan lokacin ya isa shiga makarantar boko.
Ya fara da hadejia junior elementary school dake dalla wanda a yanzu ake kira
Abdulkadir primary school a shekarar 1953-1957 a garin hadejia.

Bayan ya kammala wannan makarantane ya samu shiga middle school a cikin shekarar 1957-1959, daga nan bayan kammala middle
school ya koma makarantar horan malamai ta wudil/bichi teachers collage a shekarar 1960-1965.

Bayan kammala wannan karatune ya samu zama headmaster a garin gabas primary school a shekara ta 1966-1971, ya koma karin karatu a advance teachers collage zaria a cikin shekara ta 1971-1974 wanda ya samu certificate in education (NCE).

Bayan kamamala (NCE) bai tsaya ba domin samun degree na farko a fannin physical Health Education (PHE) wanda ya kammala a 1975-1978 ABU Zaria.

Yayi hidimar kasa (NYSC) a federal advance teachers collage dutsinma katsina state daga 1978-1979.

Wasu ayyuka da yayi: (1) mataimakin
shugaban wasannin motsa jiki gwamnatin tarayya (NSSF) 1985-1989 (2) wakili a hukumar ilimi mai zurfi ta jami'ar Ahmadu
bello dake zaria 1988-1991 (3) wakilin tantance jarabawar dalibai na kasashen africa 1995. (4) shugaban wasannin motsa
jiki na makarantun jihar jigawa.

Mukaman da ya rike: (1) shugaban
makarantar primary ta garun gabas.(2) jami'i mai kula da shiyar kudu maso yamma wadda take birnin kudu a jihar kano (3) mataimakin
shugaban kwalejin makarantar horarda malamai dake garin hadejia (4) mataimakin jami'in ilimi na shiyoyin kananan hukumomin gezawa, da minjibir a jihar kano
(5) shugaban makarantar sakandiren jeka ka dawo dake kazaure (6) shugaban kwalejin
horar da malamai ta garki. Da sauransu.

Jarman hadejia ya bar aiki ranar 30th ga watan oktoba, 2001 a matakin aiki na 16/17.
Bayan rasuwar marigayi jarman hadejia Alh. Usman sambo na (2) a ranar Asabat 4 ga watan december 2010, maimartaba sarkin
hadejia Alh. Adamu Abubakar maje Con, ya nada ALH. ABBA SAMBO a matsayin JARMAN HADEJIA na (3) kuma Dan majalisar maimartaba sarki.

HADEJIA A YAU....