Friday, January 15, 2021

Hadejia Wetlands Game Reserve.

 



INTRODUCTION OF THE GAME RESERVE

Baturiya Birds sanctuary, sometimes referred to broadly as Hadejia Wetland game reserve is a natural wetlands, located within the Sudan Sahelian region. Its stretches in a general west to east direction of Hadejia River Valley touching portion of three Local Government Areas Auyo, Kirikasamma and Guri Local Government areas in Jigawa State.The reserve was taken as Parts of Birds area of Hadejia/Nguru wetland and also as wetland of international importance (RAMSAR) 20  recently it was proposed to upgrade to a state of a national park by Nigerian national parks service (NPS).

The area of the reserve includes; the buffer zone is about 350km2 reserve support great variety of wildlife resources particulariy water game birds that are of both migratory and resident origins especially for resting activities.

HISTORY OF THE GAME RESERVE

The game reserve derived its name from the neighboring community of meaning a lady from Europe or white lady this was originated some centuary back when Baturiya community was not established, the area was just a variety of wildlife resources and Europeans used to visit and camp at. History have indicated that in early 70's the bush around Baturiya terms of variety of wildlife species and there were a lot of pond and were rich in terms of fish, crocodiles, monitor lizard and others aquatic animals. 

Thursday, October 6, 2016

(15) SARKIN HAƊEJIA ABUBAKAR MAJE HARUNA




Bayan rasuwar Sarkin Haɗejiya Alhaji Haruna sai aka naɗa Ɗansa Alhaji Abubakar Maje Haruna a matsayin Sarkin Haɗejiya na goma sha biyar (15), A jerin sarakunan Fulani, an naɗashi ranar Alhamis 30/august/1984. Sai akayi Sarki mai farin jini da hakuri da son mutane, a wajen kyauta kuwa ya kasance mai Alheri tun yana ƙaraminsa. Sarkin Haɗejiya Abubakar kafin zamansa sarki yayi Ayyuka da dama, sannan ya kasance Ɗan kasuwa. 

A zamaninsa an samu sauye sauye da dama a ƙasar Haɗejiya, musamman Ɓangaren Ilmin Addini dana zamani Kasuwanci da siyasa. Sarkin Haɗejiya Abubakar Maje ya halarci makarantu da dama inda ya fara halartar makarantar Elementary dake Unguwar Dallah a shekarar 1945, sannan ya tafi makarantar Middle School dake Unguwar fantai a shekarar 1949 zuwa 1952. Haɗejia A yau.

Sarkin Haɗejiya Abubakar ya tafi makarantar T.T.C. Maru dake a Lardin Sokoto a wancan lokacin, ya fara a cikin shekarar 1953 zuwa 1956. Sarkin Haɗejia Abubakar ya koma makarantar horar da ma’aikata dake Potiskum ta jihar Borno, wadda yanzu take a jihar Yobe. Kuma ya fara aikin gwamnati a matsayin Malamin Hakimi a Gundumar Bulangu, sannan ya riƙe muƙamin Magatakarda a majalissar Sarki. Saboda iya mu’amala da son jama’a sai yazama duk inda ka ganshi bazaka ganshi shi kaɗai ba sai da jama’a, hakan ya bashi nasarar gogewa wajen tafiyar da shugabancin jama’a. Haɗejia A yau.

A zamaninsa an samu ci gaba da yawa a ƙasar Haɗejia ta kowane fanni na rayuwa, musamman zaman lafiya da Kwanciyar hankali, sannan an samu bunƙasar garin Haɗejia wajen gine ginen zamani da gina sabin Unguwanni. A zamaninsa aka rushe ƙofar Garin Yamma da ta Arewa aka Gina sabi domin dacewa da zamani sannan aka sake gina Sabi guda uku, an gina ɗaya a Kusa da Kadime ɗaya kuma an ginata a hanyar Gumel da kuma hanyar Nguru. A zamaninsa an gina sha tale-tale (Round about) guda biyu ɗaya a yamma da kofar garin yamma, ɗaya kuma a Titin Tashar mota tsohuwa, sannan anyi sababbin hanyoyin mota a ciki da wajen Haɗejia. A zamaninsa....... Hadejia A yau! A duba littafin Fulani da mulkinsu na Ismaila A Sabo.

HADEJIA A YAU!

Friday, September 23, 2016

HADIN GWUIWA DA TAIMAKEKENIYA. Daga Abdullahi Matashi...



A bisa dabi’a kowane mutum yana da wata baiwa da ya kebantu da ita, kuma kowane mutum yana bukatar taimakon sauran mutane domin ya kai ga kamala da ci gaba.

Hadin gwuiwa abu ne da ke da tasiri matuka wajen ci gaba da cin nasara ga daidaikun jama’a da kuma al’umma baki daya. Allah Ya halicci mutum da dabi’ar zaman tare, Saboda haka a bisa dabi’a yana ta kokawar warware mishkiloli ne na rayuwa tare da sauran mutane ‘yan-uwansa.

Dabi’a da kuma bukatun mutum
su kan haifar masa da mishkiloli
dabam-dabam, dan haka shi ko
yaushe karen barar mishkiloli ne
masu tsanani. A cikin wannan hali na tsanani da bala’i ba zai taba koshi daga taimakon wadansu ba. A bisa wannan dabi’a da larura ne ayyukan da suka rataya a wuyan jama’a na kowace suka sha bam- bam. Taimakon da mutum guda
zai ba wa al’umma kome kankantarsa zai taimaka wajen
cigaban al’ummar da kammala
rayuwarta.

Tunda yake halayyar al’umma
ta ginu ne a jikin daidaikun mutane, to muna iya kamanta al’umma da bangarorin jikin mutum. Kamar yadda jikin mutum ya kunshi gabobi
dabam-dabam wadanda ke da alaka da juna wajen dorewar rayuwar mutum. Tilas ne kowace gaba ta gudanar da aikin da aka dora mata ba tare da ketare haddinta ba, haka nan al’umma ma an gina ta ne da
daidaikun mutane kazalika
dorewar al’umma yana bukatar
kowa ya san aikin da ya rataya
a wuyansa kuma ya aikata shi
iyaka karfinsa da iyawarsa.

Lalle ne kowa ya yi amfani da abin da ya mallaka na dukiya da hazaka dan tafiyar da al’umma da kyautata ta da habaka ta tare da tsayawa a kan iyakar aikinsa da aka dora a wuyansa gwargwadon fannin aikinsa da karfinsa. Dukda haka kuma ana iya samun kwanciyar hankali da zaman lafiya da jin dadi, a kuma yi galaba akan mishkilolin rayuwa ne a al’umma idan akwai kaunar hadin gwiwa a tsakanin mutane. Ta hanyar taimakon juna ne kawai rayuwa za tayi zaki, bishiyarta kuma za tayi ‘ya’ya har a samu a ja ragamar rayuwa zuwa gaba.
ABDULLAHI MATASHI...

Tuesday, July 28, 2015

Hadejia A yau.

A satin da ya gabata ne mai girma gwamnan Jihar Jigawa Alh. Badaru Abubakar,  ya sanar da Daga darajar Bubbar Asibitin Hadejia zuwa Specialist Hospital. Sannan ya daga darajar Asibitin Birniwa zuwa General Hospital,  kasar Hadejia tana da kananan hukumomi guda takwas da gundumomin Hakimai Ashirin da biyar,  amma a baya suna  amfani ne Bubbar Asibiti guda daya kafin zuwan gwamnatin Sardauna.

Da yake nasa jawabin mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar ya bayyana godiyarsa ga gwamnan Jihar jigawa, a madadin Al'ummar masarautar Hadejia,  kuma ya tabbatar da baiwa gwamnati hadin kai da goyon baya domin yiwa Al'umma aiki.

Da yake maida jawabi Gwamnan. Na jigawa ya bayyana Al'ummar kasar Hadejia da cewa sune silar zammansa gwamna a jigawa, domin sune  wadanda suka bada kaso mafi girma a kuri'ar da ta kaishi ga zama gwamna..  Gwamnan yace gwamnati zata ci gaba da cika Alkawurran da ta dauka lokacin yakin neman zabe.

Wednesday, June 10, 2015

AN ZABI SABON SHUGABAN MAJALISSAR DOKOKIN JIHAR JIGAWA.


AN ZABI SABON KAKAKIN MAJALISSAR DOKOKIN JIHAR JIGAWA DA MATAIMAKINSA.
A yau ne ake rantsar da sabuwar majalissar dokoki a Jihar Jigawa, bayan da aka rantsar da 'yan majalissar kuma sun gabatar da zaben kakakin Majalissar da mataimakinsa, Wanda aka zaba din dai a Matsayin Kakakin Majalissar shine.... Hon. Idris Garba Kareka daga karamar hukumar Jahun. Dan majalissar dokoki ta jiha mai wakiltar Karamar hukumar Gumel Hon. Sani Isyaku Abubakar ne, ya gabatar da Sunan Idris Garba a matsayin wanda yake goyon baya ya shugabanci majalissar, yayinda kuma ya samu goyon baya ga Dan majalissa mai wakiltar Kiri kasamma Hon. Aliyu Muhammad Aliyu, sai sauran 'yan Majalissar suka Amince da hakan ba tare da hamayya ba.

Haka kuma An zabi Hon. Ahmed Garba (MK) mai wakiltar Hadejia, a matsayin mataimakin kakakin majalissar Jiha, shima dan majalissa daga mazabar Birnin kudu ne ya gabatar da sunansa, daga bisani ya samu Amincewar sauran 'yan majalissar. Allah ya basu ikon sauke nauyin da aka dora musu.

NOMA KIWO DA KASUWANCI A JIHAR JIGAWA...

trbidi="on">
Daga Suleiman Ginsau.
(Kashi na daya 1)
Kamar yadda kididdige ya nuna a shekarun baya da suka wuce, noma, kiwo da kasuwanci su ke da sama da kashi 70% na tattalin arzikin JAHAR JIGAWA. Amman Gwamnatin data gabata bata kula da harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci ba a wannan Jiha ba.

Wanda hakan yasake haifarda rashin aikin yi da Talauci da Zaman kashe Wando ga Matasa a Jihar Jigawa, saka makon waccen Gwamnatin ta nuna halin ko inkula a bangaran Noma, Kiwo da Kasuwanci a Jahar.
Dan haka muna kira ga sabuwar Gwamnatin Alh. Muhammad Abubakar Badaru Talamiz, tasa Hannu sosai da sosai a harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci a wannan Jaha domin farfado da tattalin arzikin Jahar mu. Saka makon wannan Talauci dake addabar Matasa a Jahar Jigawa yasa a yanzu haka akwai Matasa sama da Mutum 780,000.00 wanda suka dada harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci domin su dogara da kansu.

Dan haka muna kira ga Sabuwar Gwamnatin (BADARU) data gaggauta taimakawa Matasan da suka fada harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci a Jahar Jigawa domin ciyar dasu gaba, da Jahar mu baki daya. Fatana dai shi ne mu sani cewar, koda zamantakewar mu ta kare da masu man-fetur, to mune muke da dawwamammen tattalin arzikin da za mu rike kanmu da shi, wato Noma na duke tsohon ciniki....... Daga Suleiman Ginsau.

Thursday, May 14, 2015

YAN GUDUN HIJIRA...



YAN GUDUN HIJIRA!
Tun a lokacin da rikicin Boko Haram ya Addabi jihohin Borno da Yobe aka samu watsuwar 'yan gudun hijira a wasu sassa na Nigeria, ciki harda jihar Jigawa, kuma akasarin wadannan 'yan gudun hijira zakaga Mata ne da kankanan yara wadanda mafiya yawa suna a kasar Hadejia da kasar Gumel. A lokacin da suka fara zuwa wadannan yankuna saboda basu da abinda zasuyi dole wasu daga cikinsu suke bin masallatai da majlissai domin neman abinda zasuci abinci da yaransu. Abin tausayi zakaga yara da basu fi shekara 7 zuwa 10 ba suna bi kantuna da wurin zaman jama'a suna neman taimako, a kwanakin baya basuyi yawan da ya wuce kaga biyu ko uku ba a kullum amma yanzu abin sai karuwa yake wanda a kalla sai kaga goma zuwa sama a rana daya da mata da kananan yara abin tausayi. zaka gansu a kofar masallatai da kasuwa har da Bankuna wurin layin Atm. Dole mumini mai Imani ya tausayawa rayuwar wadannan bayin Allah domin ba a son ransu suka bar gidajensu da 'yan uwansu suka zo suke yin Bara ba! Saboda yawan kwararowarsu yasa jama'a sun fara kosawa ganin abin ya zama ba na kare ba, yanzu kullum a baka gansu a gidanka ba kaga biyar ko shida.

MASU HANNU DA SHUNI....

Hakika Masu hali sai sunyi amfani da damar da Allah ya basu wajen taimakon wadannnan bayin Allah da muhalli da Sutura da Abinci, da kuma kula da rayuwarsu musamman kananan yaran. yana da kyau masu hali su ware wani abu daga cikin Dukiyarsu don taimakon wadannan bayin Allah a matsayin Sadakatul-jariya.

GWAMNATI MAI JIRAN GADO...

Koda yake bani da masaniya game da yunkurin da Gwamnatin Jigawa tayi game da wadannan bayin Allah, kuma ban taba ganin wani wuri da aka ware don 'yan gudun hijira ba zanso in bada shawara ga Gwamnati mai jiran Gado, A karkashin mulkin ko jagorancin Jam'iyyar Apc, dasu fara duba wannan Matsalar ta 'yan Gudun Hijira kafin su fara Aiwatar da kowane Aiki domin ceto rayuwar wadannan Mata da kananan yara daga yin Bara, wanda hakan ya fara jefa wasu daga cikinsu zuwa ga halaka. An fara samun rade radin wadannan mata 'yan gudun hijira sun fara yin Arangama da wasu gurbatattun mutane suna yin lalata dasu suna basu kudi, har ma ance wasu da yawa sunyi cikin shege Allah ya kiyaye! Abin takaici sai kaga idan 'yan Hisbah suka kama mace tana lalata in suka bincika sai kaga 'yar gudun hijira ce. Kasan Dalilin da yasata cikin wannan hali?

SHAWARA GA GWAMNATI....

Ina bada shawara ga Gwamnati mai jiran gado da suyi la'akari da wannan matsalar domin su san ta yadda zasu bullowa wannan Al'amari, ya kamata Gwamnati ta samar musu mahalli na wucin gadi sannan ta sanya yaransu a Makaranta don ceto rayuwarsu. kuma Ina baiwa Gwamnati Shawara da ta sama musu sana'oi domin su dogara da kansu. misali Gwamnati zata iya amfani da makarantar koyon sana'a don koyawa Matan yanda ake yin SABULU, SAKA, DINKI,Da sauransu. Daga karshe ina Rokon Allah da kar ya nuna mana makamanciyar wannan Bala'i da zai sa mutum ya bar gidansa da iyalinsa ya tafi wani wuri yana yin abinda ko a Addini yana daga cikin Abu mai Kaskanci. Allah ka zaunar da kasarmu da Jiharmu lafiya.

Ismaila A Sabo Hadejia.
13/may/2015.

posted from Bloggeroid

Thursday, March 26, 2015

TAKOKO GARIN SARKI BUHARI...

TAKOKO GARIN SARKI BUHARI...



Garin Takoko yana daya daga cikin garuruwan Tarihi a Masarautar Hadejia, kuma yana Arewa da garin Mairakumi wanda take karkashin karamar hukumar Mallammadori, Takoko tana karkashin Mulkin Hakimin Garungabas. A lokacin da aka cire Sarkin Hadejia Buhari daga Sarauta ya koma garin Takoko da zama shi da Mutanensa inda kuma anan ne ya zauna tsawon lokaci yana kai hare hare ga kasar Gumel, Damagaram da wasu sassa na yankin Gorgaram (Bade). A zamansa na wannan gari ya samu goyon baya daga Daular Shehun Borno da kuma Machina, sakamakon karesu da yayi daga hare hare daga Mayakan Damagaram.

Bayan cireshi daga mulki da akayi ya koma Takoko Sarkin Hadejia Buhari ya zama Barazana ga Sarakunan Daular Usmaniyya, domin suna tunanin idan aka barshi a wannan gari to Daular Borno zatayi Amfani da karfin mayakansa ta rusa Daular Usmaniyya. Dan haka sai sukayi shawarar suje su yakeshi su kama shi kokuma su kashe shi, sai aka hada mayaka daga kano, katagum, Bauchi, Zamfara da sauransu.

YAKIN TAKOKO:-
Bayan an nada Ahmadu a matsayin Sarkin Hadejia, sauran Magoya bayan shi Buhari sai suma suka bar Hadejia suka koma Takoko inda Buhari yake suka zauna tare. Sarkin Hadejia Buhari anan ya zauna tsakanin Takoko da Shafowa a Arewacin Hadejia da mutanensa kuma yake tafiyar da wannan yankin. Kuma iyakar Hadejia ce da Damagaram da Machina ta Arewa maso Gabas wato yankin Niger da kuma Borno. Kuma Buhari ya bada Gudun mawa sosai a wannan Yankin wajen karesu daga barazanar mayaka, kuma a wannan zama da yayi a Takoko Buhari ya samu kyakkyawar dangantaka da Sarkin Machina da kuma Shehun Borno Umar wanda ya mulki Borno a wannan shekara (1835-1880) wannan dangantaka ta karawa Sarki Buhari kwarewa a yake yake.

(Bishiyar da Sarki Buhari yake hutawa, tana nan a gabas da garin Takoko).


A shekarar 1851, Sarkin Musulmi Alu Bubba yayi shirin ya dauki matakin Karshe akan Buhari, saboda yana tunanin Shehun Borno zai iya amfani da Buhari ya rusa Daular Sokoto saboda ya zame musu Barazana a Arewa Maso Gabas.
A wannan lokacin kuma Dan Galadiman Sokoto ya hada Mayaka daga Hadejia,Kano,Katagum,Misau da Jama'are zuwa Takoko.

A wannan lokacin kuma Buhari da mutanensa sun fita kudu da garin shafowa a lokacin Sarkin Machina ya kawowa Buhari ziyara a garin Takoko shida Jarumansa.
A lokacinda Dan galadiman sokoto suka fito don su yaki Buhari sai ya zabi Sarkin Jama'are Samboli ya jagoranci Mayakan, saboda shi ya fisu sanin Yankin.

A ranar da zasu yaki Buhari kuma a ranar Buhari ya shirya mamaye Garuruwan da suke kudu da Hadejia, sai aka hadu a Garin Shafowa. Yayin da aka hadu aka gwabza fada Buhari yaci Galaba a kansu duk suka gudu, Sarkin Hadejia Ahmadu yayi kokarin ya Gudu Kasar Kano amma sai Barde Risku ya bishi ya Kashe shi.

Bayan Yakin Takoko yazo karshe kuma an kashe Sarkin Hadejia Ahmadu Amma ba'a son ran Buhari ba kuma aka masa Sallah aka kaishi Hadejia aka binne shi, sannan sai Buhari ya koma Hadejia yaci gaba da Mulki. Sakamakon wannan yakin, dangantaka ta sake baci tsakanin Hadejia da Sokoto, kuma Sarkin Musulmi yaki yarda da ya nada Buhari Sarkin Hadejia. Sai ya nada Tukur Na yayari, kanin Sarki Ahmadu kuma yace ya zauna a Mashama a Kasar Katagum a Matsayin sarkin Hadejia ya Gaji dan'uwansa Ahmadu. Amma Tukur bai yarda ya zama Sarkin Hadejia ba saboda yana tsoron Buhari, sai yaga bazai iya yin haka ba. Kuma saboda Gudun kar Buhari ya kasheshi sai Tukur ya Gudu daga Mashema yayi kaura zuwa Kano Lokacin Sarkin Kano Usman Na1(1846-1855) Sai aka Turashi ya Mulki Yayari a Kasar Birnin Kudu. (Yayarin Tukur) Tukur ya zauna acan Har zuwa lokacinda ya Mutu 1909. Buhari kuma yaci gaba da mulkin Hadejia yana kai hare hare a matsayin Jihadi Har saida yakai Gabasawa,Sankara,Ringim da Kuka kwance A Arewa maso yamma. A Kudu saida ya mamaye Kununu,Takalafiya, Kafin baka, Doma, Ruba, Itas da Kwanda. A Gabas kuwa saida ya Mamaye Babuwari, Kazura, Dawah, Gatare da Margadu. Saida Sarki Buhari ya fadada kasar Hadejia tafi Ko ina fadin Kasa a karni na19.

Saturday, January 31, 2015

HISTORY OF BAKIRIN HADEJIA...

HADEJIA A YAU!
BY: S. Ginsau...


Bariki is a Hausa corruption of the English work barrack, The Bariki in Hadejia town is an old Government Reserved Area (G.R.A.) which contains some important colonial structures. It is located in the eastern part of Hadejia town, at the outskirts of the town, about 2km from the Emir's palace. Bariki was built in 1905 mainly to serve as a new base for the British: specifically,as the barracks of the "B" and "C" Company of the imperial army - the Royal West African Frontier Force (RWAFF) - which later invaded and occupied Hadejia in 1906. After the establishment of colonial rule, bariki became the permanent
residence of the divisional officer (D.O) in charge of the Northern Division, His office was also established there. Other British colonial officers such as the divisional medical officer and the works engineer had their residence and offices located there.

The colonial structures at bariki-were initially built with mud blocks, However, after the consolidation
of colonial rule, the mud-buildings were replaced with that of burnt bricks which were manufactured at filin birki, also in Hadejia town, in the early 1930s. After independence in 1960, bariki continued to serve as the residence and office of the (D.O) and other senior government officials. The D.O.'s office also became the first Hadejia Local Government Secretariat, after the
1970 local government reforms.

The colonial structures at bariki-were initially built with mud blocks. However after the consolidation of colonial rule, the mud-buildings were replaced with that of burnt bricks which were manufactured at filin birki, also in Hadejia town, in the early 1930s. After independence in 1960, bariki continued to serve as the residence and office of the (D.O) and other senior government officials. The D.O.'s office also became the first Hadejia Local Government Secretariat, after the
1970 local government reforms.HADEJIA A YAU!

Monday, January 26, 2015

Saturday, January 10, 2015

TARIHIN RAYUWAR ALH. SHU'AIBU HARUNA.


ALHAJI SHU'AIBU HARUNA HADEJIA.
An haifi Alh. Shu'aibu Haruna a cikin garin Hadejia a shekara ta 1-february 1954, yayi makarantar firamare a Matsaro firamare a shekarar1961-1967, yayi makarantar sakandire ta KEDC dake Kano a shekara ta 1969-1974, sannan yayi N. C. E a ATC/ABU Zaria yayi (Degree) a ABU Zaria a inda ya karanci B. ed a Social Studies a shekara ta 1980-1982, Sannan yayiwa kasa shidima wato (NYSC) a Kwara State a shekarar 1979-1980.

Daganan yayi aikin koyarwa a Auyakayi Auyo LGA, a shekara ta 1974-1975, daganan ya koma Bichi Kano State inda yayi aikin koyarwa a shekara ta 1979-1980, Sannan ya rike mukamin (Principal) a Garo dake Kabo LGA a Kano State, a shekara ta 1982-1986, Alh. Shu'aibu Haruna ya sake rike mukamin (Principal) bayan ya koma Kiru LGA Kano State da aikin koyarwa, a cikin shekarar 1986-1991, Sannan yasake rike matsayin (Principal) a Danbatta LGA Kano State a shekara ta 1991-1992, Sannan ya sake rike da matsayin (Principal) a Kaugama LGA Jigawa State, a shekara ta 1992.

Bayan Alh. Shu'aibu Haruna Hadejia ya gama aikin koyarwarsa lafiya cikin nasara da fatan alkairi da abokan aikinsa suka masa, ya rike matsayin (Director General Ministry of Land & Regional Planing Jigawa State) a shekara ta 1992-1993. Sannan ya sake rike matsayin (Dirctor General Budget & Planing Jigawa State) 1993-1994. 

Alh Shu'aibu Haruna Hadejia, ya rike matsayin (Coucilor Hadejia LG Works & Housing) a shekara ta 1994-1996, Sannan ya Zama  (Member Constitutional Amendement) 1999.
Sannan (Chairman Hadejia World Bank Project) sannan (Asst. Sec. Movement for the creation of Hadejia State). Alh. Shu'aibu Haruna gogegge ne a fagen siyasa ya fara harkar siyasa a 1979. NEPU, PRP, NPN, NCPN, NDP, PDP, ANPP, Yanzu kuma yana APC, Kuma (National Delegate) har zuwa yanzu. ganin irin wannan godewa tasa da hakuri irin nasa yasa mutanen Hadejia
suka Tsayar da shi dan Takarar (National House of Assembly) a 2003, NDP. Mai wakiltar Hadejia Auyo da K/Hausa. Alh. Shu'aibu Haruna babban dan kasuwa ne kuma manomi ne, shine mutum na farko da ya fara kawowa kasar Hadejia cigaban da babu wanda ya kawo kasar Hadejia wato Kamfanin Leda mai suna(NAKOWA PLASTIC
LTD) wanda ya samar aiki ga matasan kasar Hadejia, sanadiyyar daukansu aiki da yayi a Kamfaninsa, wanda yanzu sama da mutum 250 suna aiki a karkashin sa, sannan ya
kawo babban cigaba a Harkokin samar da Wayoyin Hannu wato (Handset).Yana da shagunan da ake siyar da wayoyin hannu da dama a cikin garin Hadejiya, wanda mutane sama da 150, suna aiki a shagonan sa. Sannan (Chairman Nakowa Plastics Ltd) & (Pressident Jigawa Chamber of Commerce Mine & Agriculture.

Alh. Shu'aibu Haruna Hadejiya mutum ne mai hakuri da juriya da sanin yakamata. Mutanan Kasar Hadejiya suna maka fatan alkairi Allah ya daukaka rayuwarka Allah ya taimaki zuri'arka baki dayansu. Allah sauran mutanan kasar Hadejia zasuyi koyi da irin halinka. Allah yasake buda maka kasake kawomana wani cigaban kasar Hadejia wanda mutane zasuna karuwa da ita. Amin.

HADEJIA A YAU!

Saturday, December 20, 2014

ZIYARA DA AMFANINTA.

a.

r">
Ziyara wani Nau'i ne na zumunci wanda mutane suke aiwatar da ita domin sada zumunci ga 'yan'uwa da abokan Arziki. zumunci wata irin halayya ce ta kwarai wacce ke sadar da dangantaka ta nasaba tsakanin ’yan'uwa ko bare. Zumunci ne ke kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali da fahimtar juna tsakanin al’umma.

Ta hanyoyin da mutum zai bi ya inganta zumunci shine, kaiwa ziyara ga 'yan'uwansa kamar kaka, uba kokuma kanin mahaifi ko kanin mahaifiya da sauransu. Ta haka ne mutum zai gane irin yadda Alaqarsa take da 'yan uwansa na nesa ko na kusa. Haka kuma kowa yana da iya kimar zumuncin da zai gudanar a tsakaninsa da wani. Kamar yadda Hausawa suka ce zumunta a kafa take, to wannan gaskiya ne,domin
kuwa daya daga cikin manyan ginshikan zumunta shi ne ziyartar juna. Idan ka kula da zumunci shike sa mutum ya niki gari zuwa gidan abokinka ko wani dan'uwanka, ko bare musamman domin ganin yadda yake. Wannan ziyara kawai, ita ke haddasa kauna da mutunci mai dorewa a tsakanin al’umma.

A shekarun baya kamar shekara kamar goma zuwa sama,saboda muhimmancin ranar Juma'a,iyaye sukan je da 'ya'yansu gidajen 'yan'uwansu da Abokan Arziki domin gaisawa wanda hakan yana nuna ana nusar da yara ne da kaiwa ziyara ga 'yan uwansu. Harma yara suke kiran wannan ziyara da yawon Juma'a. Amma saboda shagaltar da zuciya irin ta shaidan tasa wannan kyakkyawan Aiki na ziyara ya fara ja baya ga yara harma da manyan a wannan zamani,domin shi bubba yana tunanin ai in yaje zai bada kudi, sannan yaro yana tunanin kar yaje ba'a bashi kudi ba.

Wednesday, December 3, 2014

TAKAITACCEN TARIHIN HASHIM UBALE YUSUF..

Hadejia A yau!

An haifi Hashim Ubale Yusufu a Garun Gabas da ke cikin yankin Karamar Hukumar Mallam Madori ta yanzu, A ranar 21 ga Satumba na shekarar 1956. Ya fara karatunsa a makarantar firamare a nan Garun Gabas inda ya fita da kyakkyawan sakamako a matsayin dalibi mafi kwazo da hazaka Daga nan ya wuce zuwa Sakandaren gwamnati dake Birnin Kudu inda ya yi karatu daga 1969 zuwa 1973, lokacin da ya rubuta jarrawar makarantun sakandare ta Afirka ta Yamma wato WASC.

Ya halarci Makarantar Koyon ilimi mai zurfi ta Kano, wato College of Advanced Studies daga 1973 zuwa 1975, inda ya fita da babbar takardar shaida, wato Higher School Certificate. Daga nan kuma ya sami shiga jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria inda ya yi karatun digiri a fannin ilimin harhada magunguna (wato pharmacy) wanda ya gama a shekarar 1981.Bayan ya kammala karatun jami-a, sai sai ya tafi aikin bautar kasa a jihar Imo inda aka tura shi Federal Polytechnic da ke garin Afikpo -Okposi inda ya yi aiki a matsayin mai bayar da magani na wannan makarantar da kuma koyar da darasin chemistry daga 1982 zuwa 1983.Hashim ya fara aiki tun daga matakin karamin ma'aikaci inda a tsawon shekaru ya taka matakai daban daban har zuwa matsayin darakta a hukumar kula da tsaftar abinci da magunguna a Nigeria, da kuma bubban sakatare wato permanent secretary.

Ya fara aiki a shekarar 1974 a matsayinsa na Mataimakin Jami'in gandun daji a karkashin sashen kula da gandun daji na tsohuwar Jihar Kano, sannan daga bisani ya canja aiki zuwa bubban Asibiti na Kano (wanda aka fi sani da asibitin Murtala a yanzu) inda yayi aiki amatsayin jami'i mai bada magani na wucin-gadi a cikin shekarar 1981 da 1982, inda kuma a shekarar 1983 aka daukeshi aiki a karkashin Sashen Kula da ayyukan lafiya kuma aka tura shi Asibitin Murtala da ke Kano a matsayin Jami'in bayar da magani mai daraja ta daya. Daga 1985 zuwa 1987, ya yi aiki a cibiyar sayar da magani ta Lafiya Pharmacy dake garin Hadejia, wadda ta kasance daya daga cikin cibiyoyin sayar da magani da aka bude a wancan lokacin. Bayan daukar lokaci yana aiki karkashin gwamnati,sai ya tsallaka zuwa ma'aikatu masu zaman kansu inda ya yi aiki a kamfanonin sayar da magunguna na NAMCO da kuma ANHEL das u ke cikin binin Kano daga 1987 zuwa 1989. Haka nan ya yi aiki a da hukumar bada tallafin cigaba ta kasar Amurka wato USAID a matsayin jami’in gudanar da ayyuka na kasa karkashin shirin Inganta Lafiyar Iyali (wato Family Health Services).

A shekarar 1989, ya rike mukamin Mai bada shawara a gandun daji na tsohuwar Jihar Kano, sannan daga bisani ya canja aiki zuwa Babban Asibiti na Kano (wanda aka fi sani da asibitin Murtala a yanzu) inda ya yi aiki a matsayin jami'i mai bada magani na wucin-gadi tsakanin 1981 da 1982, inda kuma a shekarar 1983 aka dauke shi aiki karkashin Sashen Kula da ayyukan lafiya kuma aka tura shi Asibitin Murtala da ke Kano a matsayin Jami'in bayar da magani mai daraja ta daya.

Wednesday, October 29, 2014

HADEJIA TOWN WALLS AND GATES.

BY: SULEIMAN GINSAU HADEJIA A YAU!HADEJIA TOWN WALLS AND GATES "Hadejia was a large town with 5 town gates and excellent walls about 30ft (9.14m) high, and 30ft (9.14m) thick " (Captain Philips 1909)

Hadejia Town walls had a long history dating back to the pre-jihad period. The walls were built to provide security to the people, and to serve as fortification against external invasion. Though mostly in ruins now, with a great proportion having completely disappeared, the walls were intact up to the time of the colonial invasion in 1906. Hadejia A yau!

The construction of the walls was done by direct labour using local building materials. Over the years, the walls have been taken subjected to several phases of development. Expansions and reinforcements were made to accommodate a growing population or to enhance security against attack by powerful enemies. The walls were invariably complimented by gates whose history could be linked to that of the walls. The gates provided the only entry points into the town. They were made extremely strong, thus making it very difficult for an enemy force to break into the town through them. Hadejia A yau.

The gates were manned by gate-keepers or porters (sarakunan kofa) appointed by the Emir. These keepers used to close the gates everyday from dusk to dawn, thus controlling the movement of people in and out of the town during these periods. Visitors or strangers were not allowed in unless with the express permission of the Emir. It was reported that one Emir ordered the gates to be left open permanently, confident that no enemy force would dare attack the town.

The first town wall in Hadejia was believed to have been built during the pre-jihad period. Though the exact date of its construction cannot be determined due to lack of proper records, its perimeter is marked by certain well-known local pits: Mai kilabo in the west, Atafi in the south, and Dallah in the East. It was said to be one mile in circumference, and had four gates. The second wall was built by Sarki Sambo in the early years of the Jihad. It was wider than the previous wall, with its perimeter approximately put at 2 miles 170 yards. It had 5 gates. The present wall, which was the third, was also built during Sambo's reign. It was built at a time when Hadejia was at the centre of a bitter rivalry between Sokoto caliphate and Borno Empire. As such it was much stronger and wider than the previous walls. An extension to this wall was later made on the Eastern side during the reign of Sarki Haruna (1865 -1885) encompassing a large space to harbor fugitives from surrounding villages in times of war.

The Habe settlement of Fantai, which hitherto was outside the wall, also became sheltered in the new extension. This brought the wall to its present size of 4miles 135yards, with 5 gates, namely:
Kofar Gabas (also known as Kofar Gwani) Kofar Arewa KofarYamma Kofar Kyalesu (also Known as Kofar Kogi) Kofar Mandara (also known as Kofar Talata) Apart from the Kofar Mandara gate, which was destroyed by the British in their attempt to gain entry into Hadejia town in 1906, the other gates are still standing in their original positions.

They have, however, undergone several modifications over the years, the latest being in1985 which saw the total re-construction of Kofar Arewa and Kofar Yamma. The Hadejia town gates now stand as historical monuments rather than as security outposts. HADEJIA A YAU BY: SULEIMAN GINSAU -- Sent from A. Sabo note fad. HADEJIA A YAU!

Monday, September 29, 2014

TARIHIN RAYUWAR GALADIMAN KANO A TAKAICE! Alhaji Tijjani Hashim.

Hadejia A yau!<p>An haifi Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim a cikin garin Kano, a shekarar 1932. Mahaifinsa shine Turakin kano Hashim dan sarkin kano Abbas jikan sarkin Kano Ibrahim Dabo. Ya fara karatun Elementary  a garin Bebeji a cikin shekarar 1944. sannan ya shiga makarantar Middile ta Kano inda ya kammala a  shekarar 1951.

A shekarar 1952 Galadiman kano ya fara aiki a  hukumar N. A. (Native Authority) ta Kano a matsayin Malamin Dabbobi, mai kula da tsafta da lafiyar dabbobi. A 1956 aka zabe shi  a matsayin dan majalissa mai wakiltar Sumaila a majalisar dokoki ta Arewa dake kaduna.

A zaman sa a wannan majalisa ne ya rike mukamai da dama ciki har da shugaban hukumar bada kwangila ta Kaduna sannan ya rike shugaban kwamitin tabbatar da jamiyyar NPC ta lashe zabe a lardin Sardauna. Sannan ya rike mukamin Ministan Ayyukan cikin gida na Jihar Arewa. Yayi Kwamishinan lardi mai kula Lardin Kabba wandda yana kan wannan mukamin ne sojoji suka yi juyin mulki.

Bayan ya dawo gida sai  Sarkin Kano Ado Bayero ya nada shi sarautar Dan-isan Kano kuma kansila mai kula da ayyukan gayya da taimakon kai da kai.

A cikin shekarar 1976 ne ya samu karin girma zuwa sarautar Turakin Kano da bashi kulawa da gundumar Kumbotso. sannan A 1980, ya sami canji zuwa kansila marar ofis saboda yawan  harkokinsa na kasuwanci. A shekarar 1989, ya samu karin girma zuwa sarautar Dan-iyan Kano, kuma ya ci gaba rike mukamin kansila marar ofis.

A shekarar 1992, ya samu karin girma a sarauta inda aka nadashi Galadiman Kano kuma shugaban kwamitin kudi na majalisar Sarki. A shekarar 2012 Sarki ya kara masa aikin hakimcin birnin Kano. Wannan aiki ya ke rike dashi har Allah ya masa rasuwa.

Galadiman Kano Tijjani mutum ne mai hakuri da juriya da Alkairi. Kuma yana da daraja a Idanun mtane sakamakon amfani da yayi da damarsa ya kafa mutane a Gwamnati. kuma babu inda zai nemi Alfarma a gwamnati bai samu ba, wannan tasa ake masa Laqabi da GAJERE WAN GWAMNATI.

A ranar28/september/2014, Allah ya yiwa Galadiman kano rasuwa ya rasu ya bar 'ya'ya da Matan Aure da 'yan-uwa da dama. Muna Addu'a Allah ya gafarta masa.

Friday, August 15, 2014

Thursday, March 20, 2014

TARIHIN SARAKUNAN FULANIN HADEJIA (Kashi na daya 1)

TARIHIN SARAKUNAN FULANI A HADEJIA...



BISMILLAHIRRAHMANIR'RAHIM.

. Kamar yanda aka sani kasar Hadejia ta koma karkashin mulkin fulani bayan da suka hambarar da mulkin Habawa a karni na goma sha biyar (15). Fulani sun shigo kasar Hadejia ne a farkon karni na goma sha biyar (15), a karkashin jagorancin Ardo Abdure dan Jamdoyji, sun fara zama ne a Jarmari kusa da garin Hadejia, har tsawon wani lokaci. Bayan rasuwar Ardo Abdure a shekarar (1788) sai Dansa Sarkin fulani Umaru ya yanke shawarar su dawo Rinde da zama, yamma da garin Hadejia. kuma Sarkin Hadejia na Habe Abubakar ya nada Umaru a matsayin Sarkin fulanin Hadejia a cikin karni na goma sha takwas (18).

SARKIN FULANI UMARU... Shine sarki na farko a jerin sarakunan fulanin Hadejia, kuma a lokacinsa aka samu labarin jihadin Shehu Usman Danfodiyo. A lokacinda sarkin fulani Umaru yaji labarin jihadin shehu sai yayi shawara da 'yan uwansa da suje suyi Mubaya'a da Da'awar Shehu. Sai ya tashi dan uwansa Sambo yaje ya meka mubaya'arsu ga Shehu da kuma nuna goyon baya ga da'awarsa ta Addinin musulunci.Sambo ya kai chaffarsa ga Shehu a cikin shekarar 1807-1808. A wannan shekara ne jama'a daga garuruwa daban daban sukayi mubaya'a ga shehu, musamman Fulani wadda sune suka taimaka masa wajen jaddada Addinin Musulunci a kasar Hausa.

Bayanda Umaru ya tura Sambo zuwa ga Shehu, sambo ya tafi da  kaninsa Laraima da kuma sauran fulani 'yan uwansa. Shehu ya zabi Sambo da ya zama shine shugaban jaddada jihadi a kasar Hadejia saboda dama Sambo yana daga Dalibansa. Bayan sun dawo Hadejia sukaci gaba da jaddada Addinin Musulunci a ciki da wajen kasar Hadejia.kuma dukda basu samu turjiya da yawa a cikin garin Hadejia ba, Sarkin fulani Umaru da magoya bayansa sun samu turjiya da yawa musamman a yankin Gabas iyakar Hadejia da Nguru da kuma yankin Auyo. Fulanin Hadejia sun fara jaddada jihadinsu ne a Wajen Hadejia, inda suka fara da kauyukan da suke kusa da Rinde kamarsu Akurya da kadime da sauransu


Monday, March 17, 2014

JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO (DAGA NA GABA PART FIVE 5)

TAKAITACCE TARIHIN MAIGIRMA JARMAN HADEJIA ALH. ABBA SAMBO!!

Daga Muhammad Yawale.


An haifi Alh. Abba sambo a shekara ta 1943 a cikin garin hadejia, ya fara karatun allo a matakin karatunsa na farko sannan lokacin ya isa shiga makarantar boko.
Ya fara da hadejia junior elementary school dake dalla wanda a yanzu ake kira
Abdulkadir primary school a shekarar 1953-1957 a garin hadejia.

Bayan ya kammala wannan makarantane ya samu shiga middle school a cikin shekarar 1957-1959, daga nan bayan kammala middle
school ya koma makarantar horan malamai ta wudil/bichi teachers collage a shekarar 1960-1965.

Bayan kammala wannan karatune ya samu zama headmaster a garin gabas primary school a shekara ta 1966-1971, ya koma karin karatu a advance teachers collage zaria a cikin shekara ta 1971-1974 wanda ya samu certificate in education (NCE).

Bayan kamamala (NCE) bai tsaya ba domin samun degree na farko a fannin physical Health Education (PHE) wanda ya kammala a 1975-1978 ABU Zaria.

Yayi hidimar kasa (NYSC) a federal advance teachers collage dutsinma katsina state daga 1978-1979.

Wasu ayyuka da yayi: (1) mataimakin
shugaban wasannin motsa jiki gwamnatin tarayya (NSSF) 1985-1989 (2) wakili a hukumar ilimi mai zurfi ta jami'ar Ahmadu
bello dake zaria 1988-1991 (3) wakilin tantance jarabawar dalibai na kasashen africa 1995. (4) shugaban wasannin motsa
jiki na makarantun jihar jigawa.

Mukaman da ya rike: (1) shugaban
makarantar primary ta garun gabas.(2) jami'i mai kula da shiyar kudu maso yamma wadda take birnin kudu a jihar kano (3) mataimakin
shugaban kwalejin makarantar horarda malamai dake garin hadejia (4) mataimakin jami'in ilimi na shiyoyin kananan hukumomin gezawa, da minjibir a jihar kano
(5) shugaban makarantar sakandiren jeka ka dawo dake kazaure (6) shugaban kwalejin
horar da malamai ta garki. Da sauransu.

Jarman hadejia ya bar aiki ranar 30th ga watan oktoba, 2001 a matakin aiki na 16/17.
Bayan rasuwar marigayi jarman hadejia Alh. Usman sambo na (2) a ranar Asabat 4 ga watan december 2010, maimartaba sarkin
hadejia Alh. Adamu Abubakar maje Con, ya nada ALH. ABBA SAMBO a matsayin JARMAN HADEJIA na (3) kuma Dan majalisar maimartaba sarki.

HADEJIA A YAU....

Thursday, March 6, 2014

DAGA NA GABA HADEJIAWA (Part four 4)

DAGA MUHAMMAD IDRIS

r;">


FARFESA HARUNA WAKILI...............Farfesa Wakili haifaffen kofar fadar Hadejia ne, kuma kamar yadda sunansa ya nuna mahaifinsa shi ne Wakilin kudun Hadejia [Dandalma] wato mai kula da yankin kudancin garin Hadejia.

Farfesa Wakili shi ne Farfesa na biyu a masarautar Hadejia kuma yana daya daga cikin `yan majalissar dattijai na Jami`ar Bayero ta kano kuma babban Alaramma a tsangayar tarihi ta makarantar, harwayau shi ne Mufti akan harkar tarihi a Arewacin kasar nan dominkafafen watsa labarai da dama na ciki da wajen Nijeriya suna dogara da fatawowinsa wajen warware matsalolin tarihi da suka bujuro musu.Baya da harkokinsa na cikin Jami`a Farfesa Haruna Wakili ya rike Daraktan Cibiyar Nazarin Harkokin Siyasa na Jami`ar wato MUMBAIYA dake Gidan Malam Aminu Kano a Unguwar Gwammajar kano.

" Na zaune bai ga gari ba", wanda bai sanJami`a ba, ba zai san gudunmawar Wakiliba domin a shekaru ashirin da biyar da suka gabata duk dan masarautar Hadejia da ya je Bayero ofishin Wakili ne zangonsa, shi kansa ba zai iya kididdige daliban da ya yi wa hanyar karatu a jami`a ba.

"Mai kamar zuwa kan aika" Yana cikin wannan gwagwarmaya Allah [swt] ya yi masa kwamishinan Ilmi na Jihar Jigawa. wannan mukami nasa duk Bahadeje mai hankali ba zai taba mantawa da shi ba domin baya da ci gaba a gyaran makarantu da samar da aiyuka da matasa da ya yi to kuma a lokacinsa babbar bukatarmu da muka dade muna nema ta neman babbar makaranta ta kai ga biya wato muka samu Jami`ar Kafin Hausa kuma aka gina babbar makarantaraiyukan gona ta Hadejia ta bar lungu ta dawo kan hanya.

Farfesa Haruna Wakili cikakken Bahadeje ne ba ya son raini amma yana da kishin al`ummarsa yana son ci gabansu kuma saboda daga darajar wannan masarauta shi rubutunsa ma na digirinsa na biyu akan wannan Masarauta ya yi.a takaice dai rayuwarsa akan bautawa Ilmi take.Hadejawa suna addu`a Allah Ya ba gwanin yafe gwado.



FARFESA HARUNA BIRNIWA............kamar yadda sunansa ya nuna Farfesa Haruna Birniwa haifaffen garin Birniwa ne kuma yana cikin haular masu mulkin garin.Birniwa shi ne farfesa na farko a cikin wannan masarauta kuma farfesa nabiyu a fadin Jihar Jigawa.

Gaba daya rayuwar Birniwa a kan bautawa Ilmi take domin ya kasance daya daga cikin dattawan malamai a Jami`ar Danfodiyo dake Sokoto na shekaru masu yawa kuma ya rike 'provost' a kwalejin Ilmi dake Gumel sannan ya rike kwamishinan Ilmi a wannan Jiha.

Farfesa Birniwa ya bayarda gudunmawa a fagen bayarda ilmi a Jihar nan matuka domin daruruwan mutane sun ci moriyarzamansa a sokoto domin shi 'admission' a wurinsa kamar mutum ya mari budurwa ne don haka za a ya ce wa shi ne ya budewa Hadejawa kofa a sokoto kuma bai bar sokoto ba sai da ya yi dashe.

Lokacin yana 'provost' ma masu rabo sun samu aiki a wurin.Birniwa ba harkar ilmin zamani kadai ya tsaya ba domin fakihi ne a fannin addini kuma fahintarsa da addini ta kara sa kyawawan halayensa sun kara kyautata domin mutum ne mai hakuri da gaskiya da rikon amana da saukin kai.wani abun sha`awa ga halayensa mai unguwarsa a Hadejia ya ce in dai yana gari duk yadda za a je neman ci gaba da shi ake yi. munaaddu`a Allah ya albarkaci bayansa.

Saturday, March 1, 2014

DAGA NA GABA! HADEJIAWA (PART TWO 2)


DAGA HASHIM AMAR...
MUHAMMAD (ABBAS SECRETARY)- Tsohon Sakataren kananan hukumomin Hadejia, Malam Maduri, SuleTankarkar da Guri; tsohon jami'in kula dajin dadin jama'a, a halin yanzu Akawun Majalisar dokoki ta Karamar Hukumar Guri(Clerk).

Wannan bawan Allah ya taka rawar gani wurin samar wa matasa da dama aikin yia lokacin da yake mukamin Sakatare musamman a Hadejia da Guri. Na san mutane da dama da wannan mutum ya samawa aikin yi, cikin su kuwa har da ni kaina.

HAJIYA SABUWA SHEHU- Shohuwar jami'ar ilmi, tsohuwar shugabar makarantar firamare, tsohuwar Sakatariyar ilmi ta Karamar Hukumar Hadejia; daya daga cikin mata 'yan boko na farko a Kasar Hadejia. Wannan baiwarAllah ta taimaka matuka wurin ci gaban ilmin mata a wannan yanki, ita ce ta dauki mafi yawanmata Malaman Makaranta a Hadejia.

Ta wani bangaren 'yar kasuwa ce da ta samar da aikin yi ga matasa ta wannan bangaren, ita ta kafa shagon gudanar da harkokin sarrafa na'ura mai kwakwalwa (Bussiness Centre)na farko a Hadejia. A yanzu haka 'yar kwamitin kwararru ce masu kula da aiyukan Bankin Duniya a Hadejia. Kuma ta na cikin kwamitin kula da Makarantun Firamare da Bankin duniya suka gina a Hadejia.

Wani abin sha'awa ita ta samar da filin ginin daya Makarantar (Shagari Community), ta nemi filin a hannun Karamar Hukumar Hadejia a  madadin LEA, filin yana hannun ta fiye da shekaru goma. Hajiya Sabuwa ta bayar da tsohongidan ta kyauta ga hukumar ilmi (LEA Hadejia) don gina Makaranta, gidan na unguwar Chadi. Allah Ya saka mata da alkhairi, ya yawaita mana irin ta.