Tuesday, January 15, 2013

TARIHIN RAYUWAR SIR. AHMADU BELLO (SARDAUNA) 15/01/2013.

Easily Upload Your Images To Myspace
Hadejia a yauAn haifi Alhaji Ahmadu Bello Sardaunan
Sokoto, a ranar 12 ga watan Yuni na 1910 a
garin Rabbar na jihar Sokoto dake Arewacin
Najeriya.
Kakansa shi ne sarkin Musulmi Bello, wanda
na daya daga cikin wadanda suka kafa
daular Sokoto, kuma dane ga marigayi
Mujaddadi Shehu Usman Dan Fodiyo.


Ahmadu Bello ya fara makaranta a garin
Sokoto, sannan ya wuce zuwa makarantar
horas da malamai ta Katsina.
Kafin daga bisani Sultan ya nada shi malami
a makarantar Middle School ta Sokoto.

A shekarar 1938 aka nada shi Sardaunan
Sokoto bayan da ya gaza a yunkurin da yayi
na zamowa Sultan, wato Sarkin Musulmi.
Ya kuma halarci kasar Ingila domin yin
karantu kan harkokin mulki a shekarar
1948.

Ya kuma fara shiga harkokin siyasa gadan-
gadan bayan dawowarsa daga karatu, inda
har aka zabe shi ya zamo mamba a majalisar
dokoki ta Arewacin Najeriya. Ya kuma zama
ministan ayyuka da raya kasa.
Ya kasance Firimiyan farko na yankin Arewa
daga shekarar 1954 zuwa 1966.
Sannan ya jagoranci jam'iyyar NPC ta lashe
kujeru da dama a zaben da aka gudanar
bayan samun 'yancin kai.
Bayan kammala zabe, ya zabi ya ci gaba da
kasancewa Firimiya, inda ya nada Abubakar
Tafawa Balewa ya zamo Fira Minista.

Ya taka rawa sosai wajen hada kan yankin
Arewacin kasar wanda keda kabilu mabiya
addini daban-daban, da kuma aiwatar da
ayyuka na ci gaban kasa.


An kashe Ahmadu Bello a ranar 15 ga watan
Janairun shekara ta 1966, bayan wani juyin
mulki da wasu sojoji 'yan kabilar Ibo suka
jagoranta.

1 comment:

  1. I think this is one of the most vital info for me. And i am glad reading your article.

    But want to remark on few general things, The website style is ideal,
    the articles is really great : D. Good job, cheers
    Review my site :: Tao of Badass

    ReplyDelete