Wednesday, June 10, 2015

AN ZABI SABON SHUGABAN MAJALISSAR DOKOKIN JIHAR JIGAWA.


AN ZABI SABON KAKAKIN MAJALISSAR DOKOKIN JIHAR JIGAWA DA MATAIMAKINSA.
A yau ne ake rantsar da sabuwar majalissar dokoki a Jihar Jigawa, bayan da aka rantsar da 'yan majalissar kuma sun gabatar da zaben kakakin Majalissar da mataimakinsa, Wanda aka zaba din dai a Matsayin Kakakin Majalissar shine.... Hon. Idris Garba Kareka daga karamar hukumar Jahun. Dan majalissar dokoki ta jiha mai wakiltar Karamar hukumar Gumel Hon. Sani Isyaku Abubakar ne, ya gabatar da Sunan Idris Garba a matsayin wanda yake goyon baya ya shugabanci majalissar, yayinda kuma ya samu goyon baya ga Dan majalissa mai wakiltar Kiri kasamma Hon. Aliyu Muhammad Aliyu, sai sauran 'yan Majalissar suka Amince da hakan ba tare da hamayya ba.

Haka kuma An zabi Hon. Ahmed Garba (MK) mai wakiltar Hadejia, a matsayin mataimakin kakakin majalissar Jiha, shima dan majalissa daga mazabar Birnin kudu ne ya gabatar da sunansa, daga bisani ya samu Amincewar sauran 'yan majalissar. Allah ya basu ikon sauke nauyin da aka dora musu.

NOMA KIWO DA KASUWANCI A JIHAR JIGAWA...

trbidi="on">
Daga Suleiman Ginsau.
(Kashi na daya 1)
Kamar yadda kididdige ya nuna a shekarun baya da suka wuce, noma, kiwo da kasuwanci su ke da sama da kashi 70% na tattalin arzikin JAHAR JIGAWA. Amman Gwamnatin data gabata bata kula da harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci ba a wannan Jiha ba.

Wanda hakan yasake haifarda rashin aikin yi da Talauci da Zaman kashe Wando ga Matasa a Jihar Jigawa, saka makon waccen Gwamnatin ta nuna halin ko inkula a bangaran Noma, Kiwo da Kasuwanci a Jahar.
Dan haka muna kira ga sabuwar Gwamnatin Alh. Muhammad Abubakar Badaru Talamiz, tasa Hannu sosai da sosai a harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci a wannan Jaha domin farfado da tattalin arzikin Jahar mu. Saka makon wannan Talauci dake addabar Matasa a Jahar Jigawa yasa a yanzu haka akwai Matasa sama da Mutum 780,000.00 wanda suka dada harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci domin su dogara da kansu.

Dan haka muna kira ga Sabuwar Gwamnatin (BADARU) data gaggauta taimakawa Matasan da suka fada harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci a Jahar Jigawa domin ciyar dasu gaba, da Jahar mu baki daya. Fatana dai shi ne mu sani cewar, koda zamantakewar mu ta kare da masu man-fetur, to mune muke da dawwamammen tattalin arzikin da za mu rike kanmu da shi, wato Noma na duke tsohon ciniki....... Daga Suleiman Ginsau.