Tuesday, July 28, 2015

Hadejia A yau.

A satin da ya gabata ne mai girma gwamnan Jihar Jigawa Alh. Badaru Abubakar,  ya sanar da Daga darajar Bubbar Asibitin Hadejia zuwa Specialist Hospital. Sannan ya daga darajar Asibitin Birniwa zuwa General Hospital,  kasar Hadejia tana da kananan hukumomi guda takwas da gundumomin Hakimai Ashirin da biyar,  amma a baya suna  amfani ne Bubbar Asibiti guda daya kafin zuwan gwamnatin Sardauna.

Da yake nasa jawabin mai martaba sarkin Hadejia Alh. Adamu Abubakar ya bayyana godiyarsa ga gwamnan Jihar jigawa, a madadin Al'ummar masarautar Hadejia,  kuma ya tabbatar da baiwa gwamnati hadin kai da goyon baya domin yiwa Al'umma aiki.

Da yake maida jawabi Gwamnan. Na jigawa ya bayyana Al'ummar kasar Hadejia da cewa sune silar zammansa gwamna a jigawa, domin sune  wadanda suka bada kaso mafi girma a kuri'ar da ta kaishi ga zama gwamna..  Gwamnan yace gwamnati zata ci gaba da cika Alkawurran da ta dauka lokacin yakin neman zabe.

Wednesday, June 10, 2015

AN ZABI SABON SHUGABAN MAJALISSAR DOKOKIN JIHAR JIGAWA.


AN ZABI SABON KAKAKIN MAJALISSAR DOKOKIN JIHAR JIGAWA DA MATAIMAKINSA.
A yau ne ake rantsar da sabuwar majalissar dokoki a Jihar Jigawa, bayan da aka rantsar da 'yan majalissar kuma sun gabatar da zaben kakakin Majalissar da mataimakinsa, Wanda aka zaba din dai a Matsayin Kakakin Majalissar shine.... Hon. Idris Garba Kareka daga karamar hukumar Jahun. Dan majalissar dokoki ta jiha mai wakiltar Karamar hukumar Gumel Hon. Sani Isyaku Abubakar ne, ya gabatar da Sunan Idris Garba a matsayin wanda yake goyon baya ya shugabanci majalissar, yayinda kuma ya samu goyon baya ga Dan majalissa mai wakiltar Kiri kasamma Hon. Aliyu Muhammad Aliyu, sai sauran 'yan Majalissar suka Amince da hakan ba tare da hamayya ba.

Haka kuma An zabi Hon. Ahmed Garba (MK) mai wakiltar Hadejia, a matsayin mataimakin kakakin majalissar Jiha, shima dan majalissa daga mazabar Birnin kudu ne ya gabatar da sunansa, daga bisani ya samu Amincewar sauran 'yan majalissar. Allah ya basu ikon sauke nauyin da aka dora musu.

NOMA KIWO DA KASUWANCI A JIHAR JIGAWA...

trbidi="on">
Daga Suleiman Ginsau.
(Kashi na daya 1)
Kamar yadda kididdige ya nuna a shekarun baya da suka wuce, noma, kiwo da kasuwanci su ke da sama da kashi 70% na tattalin arzikin JAHAR JIGAWA. Amman Gwamnatin data gabata bata kula da harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci ba a wannan Jiha ba.

Wanda hakan yasake haifarda rashin aikin yi da Talauci da Zaman kashe Wando ga Matasa a Jihar Jigawa, saka makon waccen Gwamnatin ta nuna halin ko inkula a bangaran Noma, Kiwo da Kasuwanci a Jahar.
Dan haka muna kira ga sabuwar Gwamnatin Alh. Muhammad Abubakar Badaru Talamiz, tasa Hannu sosai da sosai a harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci a wannan Jaha domin farfado da tattalin arzikin Jahar mu. Saka makon wannan Talauci dake addabar Matasa a Jahar Jigawa yasa a yanzu haka akwai Matasa sama da Mutum 780,000.00 wanda suka dada harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci domin su dogara da kansu.

Dan haka muna kira ga Sabuwar Gwamnatin (BADARU) data gaggauta taimakawa Matasan da suka fada harkokin Noma, Kiwo da Kasuwanci a Jahar Jigawa domin ciyar dasu gaba, da Jahar mu baki daya. Fatana dai shi ne mu sani cewar, koda zamantakewar mu ta kare da masu man-fetur, to mune muke da dawwamammen tattalin arzikin da za mu rike kanmu da shi, wato Noma na duke tsohon ciniki....... Daga Suleiman Ginsau.

Thursday, May 14, 2015

YAN GUDUN HIJIRA...



YAN GUDUN HIJIRA!
Tun a lokacin da rikicin Boko Haram ya Addabi jihohin Borno da Yobe aka samu watsuwar 'yan gudun hijira a wasu sassa na Nigeria, ciki harda jihar Jigawa, kuma akasarin wadannan 'yan gudun hijira zakaga Mata ne da kankanan yara wadanda mafiya yawa suna a kasar Hadejia da kasar Gumel. A lokacin da suka fara zuwa wadannan yankuna saboda basu da abinda zasuyi dole wasu daga cikinsu suke bin masallatai da majlissai domin neman abinda zasuci abinci da yaransu. Abin tausayi zakaga yara da basu fi shekara 7 zuwa 10 ba suna bi kantuna da wurin zaman jama'a suna neman taimako, a kwanakin baya basuyi yawan da ya wuce kaga biyu ko uku ba a kullum amma yanzu abin sai karuwa yake wanda a kalla sai kaga goma zuwa sama a rana daya da mata da kananan yara abin tausayi. zaka gansu a kofar masallatai da kasuwa har da Bankuna wurin layin Atm. Dole mumini mai Imani ya tausayawa rayuwar wadannan bayin Allah domin ba a son ransu suka bar gidajensu da 'yan uwansu suka zo suke yin Bara ba! Saboda yawan kwararowarsu yasa jama'a sun fara kosawa ganin abin ya zama ba na kare ba, yanzu kullum a baka gansu a gidanka ba kaga biyar ko shida.

MASU HANNU DA SHUNI....

Hakika Masu hali sai sunyi amfani da damar da Allah ya basu wajen taimakon wadannnan bayin Allah da muhalli da Sutura da Abinci, da kuma kula da rayuwarsu musamman kananan yaran. yana da kyau masu hali su ware wani abu daga cikin Dukiyarsu don taimakon wadannan bayin Allah a matsayin Sadakatul-jariya.

GWAMNATI MAI JIRAN GADO...

Koda yake bani da masaniya game da yunkurin da Gwamnatin Jigawa tayi game da wadannan bayin Allah, kuma ban taba ganin wani wuri da aka ware don 'yan gudun hijira ba zanso in bada shawara ga Gwamnati mai jiran Gado, A karkashin mulkin ko jagorancin Jam'iyyar Apc, dasu fara duba wannan Matsalar ta 'yan Gudun Hijira kafin su fara Aiwatar da kowane Aiki domin ceto rayuwar wadannan Mata da kananan yara daga yin Bara, wanda hakan ya fara jefa wasu daga cikinsu zuwa ga halaka. An fara samun rade radin wadannan mata 'yan gudun hijira sun fara yin Arangama da wasu gurbatattun mutane suna yin lalata dasu suna basu kudi, har ma ance wasu da yawa sunyi cikin shege Allah ya kiyaye! Abin takaici sai kaga idan 'yan Hisbah suka kama mace tana lalata in suka bincika sai kaga 'yar gudun hijira ce. Kasan Dalilin da yasata cikin wannan hali?

SHAWARA GA GWAMNATI....

Ina bada shawara ga Gwamnati mai jiran gado da suyi la'akari da wannan matsalar domin su san ta yadda zasu bullowa wannan Al'amari, ya kamata Gwamnati ta samar musu mahalli na wucin gadi sannan ta sanya yaransu a Makaranta don ceto rayuwarsu. kuma Ina baiwa Gwamnati Shawara da ta sama musu sana'oi domin su dogara da kansu. misali Gwamnati zata iya amfani da makarantar koyon sana'a don koyawa Matan yanda ake yin SABULU, SAKA, DINKI,Da sauransu. Daga karshe ina Rokon Allah da kar ya nuna mana makamanciyar wannan Bala'i da zai sa mutum ya bar gidansa da iyalinsa ya tafi wani wuri yana yin abinda ko a Addini yana daga cikin Abu mai Kaskanci. Allah ka zaunar da kasarmu da Jiharmu lafiya.

Ismaila A Sabo Hadejia.
13/may/2015.

posted from Bloggeroid

Thursday, March 26, 2015

TAKOKO GARIN SARKI BUHARI...

TAKOKO GARIN SARKI BUHARI...



Garin Takoko yana daya daga cikin garuruwan Tarihi a Masarautar Hadejia, kuma yana Arewa da garin Mairakumi wanda take karkashin karamar hukumar Mallammadori, Takoko tana karkashin Mulkin Hakimin Garungabas. A lokacin da aka cire Sarkin Hadejia Buhari daga Sarauta ya koma garin Takoko da zama shi da Mutanensa inda kuma anan ne ya zauna tsawon lokaci yana kai hare hare ga kasar Gumel, Damagaram da wasu sassa na yankin Gorgaram (Bade). A zamansa na wannan gari ya samu goyon baya daga Daular Shehun Borno da kuma Machina, sakamakon karesu da yayi daga hare hare daga Mayakan Damagaram.

Bayan cireshi daga mulki da akayi ya koma Takoko Sarkin Hadejia Buhari ya zama Barazana ga Sarakunan Daular Usmaniyya, domin suna tunanin idan aka barshi a wannan gari to Daular Borno zatayi Amfani da karfin mayakansa ta rusa Daular Usmaniyya. Dan haka sai sukayi shawarar suje su yakeshi su kama shi kokuma su kashe shi, sai aka hada mayaka daga kano, katagum, Bauchi, Zamfara da sauransu.

YAKIN TAKOKO:-
Bayan an nada Ahmadu a matsayin Sarkin Hadejia, sauran Magoya bayan shi Buhari sai suma suka bar Hadejia suka koma Takoko inda Buhari yake suka zauna tare. Sarkin Hadejia Buhari anan ya zauna tsakanin Takoko da Shafowa a Arewacin Hadejia da mutanensa kuma yake tafiyar da wannan yankin. Kuma iyakar Hadejia ce da Damagaram da Machina ta Arewa maso Gabas wato yankin Niger da kuma Borno. Kuma Buhari ya bada Gudun mawa sosai a wannan Yankin wajen karesu daga barazanar mayaka, kuma a wannan zama da yayi a Takoko Buhari ya samu kyakkyawar dangantaka da Sarkin Machina da kuma Shehun Borno Umar wanda ya mulki Borno a wannan shekara (1835-1880) wannan dangantaka ta karawa Sarki Buhari kwarewa a yake yake.

(Bishiyar da Sarki Buhari yake hutawa, tana nan a gabas da garin Takoko).


A shekarar 1851, Sarkin Musulmi Alu Bubba yayi shirin ya dauki matakin Karshe akan Buhari, saboda yana tunanin Shehun Borno zai iya amfani da Buhari ya rusa Daular Sokoto saboda ya zame musu Barazana a Arewa Maso Gabas.
A wannan lokacin kuma Dan Galadiman Sokoto ya hada Mayaka daga Hadejia,Kano,Katagum,Misau da Jama'are zuwa Takoko.

A wannan lokacin kuma Buhari da mutanensa sun fita kudu da garin shafowa a lokacin Sarkin Machina ya kawowa Buhari ziyara a garin Takoko shida Jarumansa.
A lokacinda Dan galadiman sokoto suka fito don su yaki Buhari sai ya zabi Sarkin Jama'are Samboli ya jagoranci Mayakan, saboda shi ya fisu sanin Yankin.

A ranar da zasu yaki Buhari kuma a ranar Buhari ya shirya mamaye Garuruwan da suke kudu da Hadejia, sai aka hadu a Garin Shafowa. Yayin da aka hadu aka gwabza fada Buhari yaci Galaba a kansu duk suka gudu, Sarkin Hadejia Ahmadu yayi kokarin ya Gudu Kasar Kano amma sai Barde Risku ya bishi ya Kashe shi.

Bayan Yakin Takoko yazo karshe kuma an kashe Sarkin Hadejia Ahmadu Amma ba'a son ran Buhari ba kuma aka masa Sallah aka kaishi Hadejia aka binne shi, sannan sai Buhari ya koma Hadejia yaci gaba da Mulki. Sakamakon wannan yakin, dangantaka ta sake baci tsakanin Hadejia da Sokoto, kuma Sarkin Musulmi yaki yarda da ya nada Buhari Sarkin Hadejia. Sai ya nada Tukur Na yayari, kanin Sarki Ahmadu kuma yace ya zauna a Mashama a Kasar Katagum a Matsayin sarkin Hadejia ya Gaji dan'uwansa Ahmadu. Amma Tukur bai yarda ya zama Sarkin Hadejia ba saboda yana tsoron Buhari, sai yaga bazai iya yin haka ba. Kuma saboda Gudun kar Buhari ya kasheshi sai Tukur ya Gudu daga Mashema yayi kaura zuwa Kano Lokacin Sarkin Kano Usman Na1(1846-1855) Sai aka Turashi ya Mulki Yayari a Kasar Birnin Kudu. (Yayarin Tukur) Tukur ya zauna acan Har zuwa lokacinda ya Mutu 1909. Buhari kuma yaci gaba da mulkin Hadejia yana kai hare hare a matsayin Jihadi Har saida yakai Gabasawa,Sankara,Ringim da Kuka kwance A Arewa maso yamma. A Kudu saida ya mamaye Kununu,Takalafiya, Kafin baka, Doma, Ruba, Itas da Kwanda. A Gabas kuwa saida ya Mamaye Babuwari, Kazura, Dawah, Gatare da Margadu. Saida Sarki Buhari ya fadada kasar Hadejia tafi Ko ina fadin Kasa a karni na19.

Saturday, January 31, 2015

HISTORY OF BAKIRIN HADEJIA...

HADEJIA A YAU!
BY: S. Ginsau...


Bariki is a Hausa corruption of the English work barrack, The Bariki in Hadejia town is an old Government Reserved Area (G.R.A.) which contains some important colonial structures. It is located in the eastern part of Hadejia town, at the outskirts of the town, about 2km from the Emir's palace. Bariki was built in 1905 mainly to serve as a new base for the British: specifically,as the barracks of the "B" and "C" Company of the imperial army - the Royal West African Frontier Force (RWAFF) - which later invaded and occupied Hadejia in 1906. After the establishment of colonial rule, bariki became the permanent
residence of the divisional officer (D.O) in charge of the Northern Division, His office was also established there. Other British colonial officers such as the divisional medical officer and the works engineer had their residence and offices located there.

The colonial structures at bariki-were initially built with mud blocks, However, after the consolidation
of colonial rule, the mud-buildings were replaced with that of burnt bricks which were manufactured at filin birki, also in Hadejia town, in the early 1930s. After independence in 1960, bariki continued to serve as the residence and office of the (D.O) and other senior government officials. The D.O.'s office also became the first Hadejia Local Government Secretariat, after the
1970 local government reforms.

The colonial structures at bariki-were initially built with mud blocks. However after the consolidation of colonial rule, the mud-buildings were replaced with that of burnt bricks which were manufactured at filin birki, also in Hadejia town, in the early 1930s. After independence in 1960, bariki continued to serve as the residence and office of the (D.O) and other senior government officials. The D.O.'s office also became the first Hadejia Local Government Secretariat, after the
1970 local government reforms.HADEJIA A YAU!

Monday, January 26, 2015

Saturday, January 10, 2015

TARIHIN RAYUWAR ALH. SHU'AIBU HARUNA.


ALHAJI SHU'AIBU HARUNA HADEJIA.
An haifi Alh. Shu'aibu Haruna a cikin garin Hadejia a shekara ta 1-february 1954, yayi makarantar firamare a Matsaro firamare a shekarar1961-1967, yayi makarantar sakandire ta KEDC dake Kano a shekara ta 1969-1974, sannan yayi N. C. E a ATC/ABU Zaria yayi (Degree) a ABU Zaria a inda ya karanci B. ed a Social Studies a shekara ta 1980-1982, Sannan yayiwa kasa shidima wato (NYSC) a Kwara State a shekarar 1979-1980.

Daganan yayi aikin koyarwa a Auyakayi Auyo LGA, a shekara ta 1974-1975, daganan ya koma Bichi Kano State inda yayi aikin koyarwa a shekara ta 1979-1980, Sannan ya rike mukamin (Principal) a Garo dake Kabo LGA a Kano State, a shekara ta 1982-1986, Alh. Shu'aibu Haruna ya sake rike mukamin (Principal) bayan ya koma Kiru LGA Kano State da aikin koyarwa, a cikin shekarar 1986-1991, Sannan yasake rike matsayin (Principal) a Danbatta LGA Kano State a shekara ta 1991-1992, Sannan ya sake rike da matsayin (Principal) a Kaugama LGA Jigawa State, a shekara ta 1992.

Bayan Alh. Shu'aibu Haruna Hadejia ya gama aikin koyarwarsa lafiya cikin nasara da fatan alkairi da abokan aikinsa suka masa, ya rike matsayin (Director General Ministry of Land & Regional Planing Jigawa State) a shekara ta 1992-1993. Sannan ya sake rike matsayin (Dirctor General Budget & Planing Jigawa State) 1993-1994. 

Alh Shu'aibu Haruna Hadejia, ya rike matsayin (Coucilor Hadejia LG Works & Housing) a shekara ta 1994-1996, Sannan ya Zama  (Member Constitutional Amendement) 1999.
Sannan (Chairman Hadejia World Bank Project) sannan (Asst. Sec. Movement for the creation of Hadejia State). Alh. Shu'aibu Haruna gogegge ne a fagen siyasa ya fara harkar siyasa a 1979. NEPU, PRP, NPN, NCPN, NDP, PDP, ANPP, Yanzu kuma yana APC, Kuma (National Delegate) har zuwa yanzu. ganin irin wannan godewa tasa da hakuri irin nasa yasa mutanen Hadejia
suka Tsayar da shi dan Takarar (National House of Assembly) a 2003, NDP. Mai wakiltar Hadejia Auyo da K/Hausa. Alh. Shu'aibu Haruna babban dan kasuwa ne kuma manomi ne, shine mutum na farko da ya fara kawowa kasar Hadejia cigaban da babu wanda ya kawo kasar Hadejia wato Kamfanin Leda mai suna(NAKOWA PLASTIC
LTD) wanda ya samar aiki ga matasan kasar Hadejia, sanadiyyar daukansu aiki da yayi a Kamfaninsa, wanda yanzu sama da mutum 250 suna aiki a karkashin sa, sannan ya
kawo babban cigaba a Harkokin samar da Wayoyin Hannu wato (Handset).Yana da shagunan da ake siyar da wayoyin hannu da dama a cikin garin Hadejiya, wanda mutane sama da 150, suna aiki a shagonan sa. Sannan (Chairman Nakowa Plastics Ltd) & (Pressident Jigawa Chamber of Commerce Mine & Agriculture.

Alh. Shu'aibu Haruna Hadejiya mutum ne mai hakuri da juriya da sanin yakamata. Mutanan Kasar Hadejiya suna maka fatan alkairi Allah ya daukaka rayuwarka Allah ya taimaki zuri'arka baki dayansu. Allah sauran mutanan kasar Hadejia zasuyi koyi da irin halinka. Allah yasake buda maka kasake kawomana wani cigaban kasar Hadejia wanda mutane zasuna karuwa da ita. Amin.

HADEJIA A YAU!